Gwamna Zulum Ya Yi Babban Rashi, Mai Magana Da Yawunsa, Gusau, Ya Rasu
- Mai taimakawa na musamman bangaren watsa labarai da tsare-tsare na Gwamna Babagana Zulum, Mallam Isa Gusau, ya rasu sakamakon rashin lafiya
- Yayin da kawo yanzu gwamnatin Borno ba ta fitar da sanarwa a hukumance ba, wani rahoto ya yi ikirarin cewa ya rasu a Indiya ne, wani kuma ya ce a Landan ya rasu yayin masa magani
- Gusau shine mai magana da yawun Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima lokacin da ya ke gwamnan jihar ta Borno
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Maiduguri, Borno - Rahotanni da suka fito na cewa mai magana da yawun Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno, Mallam Isa Gusau, ya rasu a wani asibiti da ke kasar Indiya.
A cewar This Day, Gusau shine mai magana da yawun Kashim Shettima, mataimakin shugaban kasan Najeriya, a lokacin da ya ke gwamna a jihar Borno. An rahoto cewa kakakin gwamnan ya shafe kimanin wata guda a wani asibiti a Indiya yana jinyar wani ciyo da ba a bayyana ba kawo yanzu.

Kara karanta wannan
Betta Edu: Gwamonin APC sun dauki mataki ana tsaka da binciken badakala, bayanai sun fito

Asali: Twitter
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A ina mai magana da yawun Gwamna Zulum ya rasu
Jaridar ta rahoto cewa Gusau ya yi numfashinsa na karshe a ranar Alhamis, 11 ga watan Janairu, a wani asibitin kwararru a New Delhi, babban birnin Indiya, a cewar wata majiya da nemi a boye sunanta.
A cewar majiyar:
"Mun rasa Isa, ya suma na kimanin kwana uku, dukkanmu muna masa addu'ar samun sauki, amma abin bakin ciki ya rasu da yamma yau (jiya) a asibiti a New Delhi, Indiya."
Ta yaya hadimin Zulum ya rasu?
This Day a cikin rahotonta ta kara da cewa marigayi Gusau bai dena yin ayyukansa ba har ma a gadon asibiti a Indiya, ta kara da cewa ya fitar da sanarwar manema labarai da dama.
Sai dai, Leadership, ta ambaci wata majiya a rahotonta da ke cewa hadimin gwamnan ya rasu a wani asibiti da ke Landan, inda ake masa magani kan wani rashin lafiya da ya dade yana fama da ita.

Kara karanta wannan
Innalillahi: Tsohon Atoni-janar a jihar Arewa ya riga mu gidan gaskiya da shekaru 81
Kawo yanzu gwamnatin jihar Borno ba ta riga ta fitar da sanarwa ba a hukumance dangane da rasuwar hadimin gwamnan, kuma ba a riga an gano ko an dawo da gawansa Najeriya ba don masa jana'iza.
Asali: Legit.ng