Yanzun nan: Babbar Kotu Ta Raba Gardama, Ta Bayyana Halastaccen Sakataren PDP Na Ƙasa

Yanzun nan: Babbar Kotu Ta Raba Gardama, Ta Bayyana Halastaccen Sakataren PDP Na Ƙasa

  • Babbar kotun birnin Abuja ta yanke hukunci kan taƙaddamar kujerar sakataren jam'iyyar PDP na ƙasa
  • Yayin yanke hukunci ranar Talata, kotun ta tabbatar da Sanata Samuel Anayanwu a matsayin sakataren PDP
  • Mai shari'a Inyang Ekwo ya kuma hana INEC karɓan wani daban a matsayin sakataren babban jam'iyyar adawa in banda Anyanwu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Babbar kotun birnin tarayya Abuja ta bayyana Sanata Samuel Anyanwu a matsayin sahihin sakataren Peoples Democratic Party (PDP) na ƙasa.

Mai shari'a Inyang Ekwo ne ya yanke wannan hukunci ranar Talata, 9 ga watan Janairu, 2024, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Sanata Samuel Anyanwu.
Yanzun nan: Babbar kotu ta raba gardama, ta bayyana halastaccen sakataren PDP na ƙasa Hoto: Samuel Anyanwu
Asali: Facebook

Ya kuma bada umarnin hana jam'iyyar PDP naɗa wani sakataren riƙo yayin da wa'adin shekaru huɗu na Sanata Anyanwu bai kare ba sai shekarar 2025.

Kara karanta wannan

Tinubu ya kira wani minista zuwa Aso Villa kan badaƙalar N438m da Betta Edu, bayanai sun fito

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar alkalin kotun, Sanatan ba zai bar kujerar sakataren PDP na ƙasa ba har sai ranar 25 ga watan Disamba, 2025 kamar yadda kundin tsarin jam'iyyar ya tanada.

Mai shari'a Ekwo ya bayyana cewa duk wani yunƙuri na hana Anyanwu yin aikin ofishinsa ya saɓawa sashi na 47 (1) na kundin dokokin PDP na 2017 wanda aka yi wa garambawul, Channels tv ta ruwaito.

Kotun ta aike da saƙo ga INEC

Bugu da ƙari, Alkalin ya hana hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta amince da kowaye aka kai mata a matsayin sakataren PDP na ƙasa in banda Anyanwu.

Kamfanin dillancin labarai (NAN) ya ruwaito cewa, a ranar 23 ga watan Nuwamba, 2023, kotun ta dakatar da PDP daga cire Anyanwu a matsayin sakataren har zuwa lokacin da zata yanke hukunci.

Kara karanta wannan

Badaƙalar N37bn: Jami'an EFCC sun titsiye tsohuwar ministar Buhari, sun tashi muhimman bayanai

Takarar da Sanata Anyanwu ya tsaya a zaben gwamnan jihar Imo ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023 ne ya hadddasa ruɗani kan kujerarsa ta sakataren PDP.

INEC ta kammala shirin zabe a Kano

A wani rahoton na daban INEC ta bayyana cewa ta kammala dukkan wasu shirye-shiryen gudanar da zaben cike gurbi na yan majalisar dokokin jihar Kano guda 3.

Kwamishinan zaben jihar, Abdu Zango, ya ce jami'ai sun shirya tsaf domin gudanar da sahihin zaɓe a watan Fabrairu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262