Akeredolu: Fitaccen Malamin Addini Ya Fadi Wanda Zai Zama Gwamnan Ondo a 2024
- Babban fasto Ifetayo Afinjuomo ya bayyana cewa wani mutum daga yankin Ileoluji/Okeigbo shine zai zama gwamna idan aka yi zaben gwamnan jihar Ondo na gaba
- Hasashen Fasto Afinjuomo na zuwa ne adaidai lokacin da Rotimi Akeredolu, gwamnan jihar Ondo ya kwanta dama
- Legit Hausa ta rahoto cewa Akeredolu, babban lauyan Najeriya, ya mutu a ranar Laraba, 27 ga watan Disamba yana da shekaru 67 a duniya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum
Ore, jihar Ondo - Babban faston da ke jan ragamar cocin Dominion Faith, Ore, Ondo, Prophet Ifetayo Afinjuomo, ya ce wani dan siyasa daga yankin karamar hukumar Ile Oluji/Okeigbo na jihar, shine zai lashe zaben gwamnan jihar Ondo a 2024.
Bai dade ba da hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ta sanar da ranar zaben gwamna a jihar Ondo.

Source: Facebook
Malamin addini ya yi hasashe kan zaben Ondo na gaba
An tsara za a yi zaben gwamnan jihar Ondo a ranar Asabar, 16 ga watan Nuwamban 2024.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Legit Hausa ta rahoto cewa wa'adin mulkin tikitin hadin gwiwa na marigayi Rotimi Akeredolu da Lucky Aiyedatiwa zai kare a ranar 23 ga watan Fabrairun 2025.
Sakon da Prophet Afinjuomo ya wallafa a shafinsa na Facebook na cewa:
"Hasashe kan 2024.
"Najeriya: lokaci ya yi da za a bunkasa.
"Zaben jihar Ondo: Na ga wani mutumin Ileoluji/Okeigbo da zai zama gwamna.
"Kasar Japan: Ku yi wa Japan addu'a, na ga an datse tutarta.
"Mutum daya: Wani sabon tafiya zai tashi daga bangaren Almasihu.
"2024 shekarar karuwata ce. Hallelujah!"
Gwamnan ya rasu ne da safiyar Laraba, 27 ga watan Disamba, 2023.

Kara karanta wannan
Aiyedatiwa: Jerin hadiman gwamna da suka yi murabus daga muƙamansu bayan mutuwa ta gitta
Diyar Akeredolu ta fatattaki yan jarida
A wani labarin, mun ji a baya cewa diyar Marigayi Rotimi Akeredolu, Ololade, ta fatattaki yan jarida da suka je daukar bayanan ziyarar ta'aziyya da manyan masu fada aji suka kai gidan tsohon gwamnan jihar Ondo a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.
Kamar yadda jaridar Vanguard ta rahoto, diyar tsohon gwamnan ta koka cewa gidan Ibadan gidansu ne mai zaman kansa ba gidan gwamnati ba.
Asali: Legit.ng
