Wike vs Fubara: Cikakkun Jerin Kwamishinonin da Suka Yi Murabus Zuwa Yanzu

Wike vs Fubara: Cikakkun Jerin Kwamishinonin da Suka Yi Murabus Zuwa Yanzu

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Rikicin siyasar jihar Ribas ya dauki sabon salo yayin da kwamishinonin Gwamna Siminalayi Fubara suka fara yasar da gwamnan sakamakon kin yin sulhu da magabacinsa kuma ubangidansa, Nyesom Wike.

Akalla kwamishinoni takwas cikin 18 ne suka mika wasikunsu na barin aiki zuwa safiyar Juma'a, 5 ga watan Disamba.

Kwamishinoni sun fara ajiye aiki awanni 24 bayan gwamnan ya rusa zauren majalisar dokokin jihar Ribas da kuma gabatar da kasafin kudinsa na sama da naira biliyan 800 ga yan majalisa hudu masu biyayya gare shi a gidan gwamnati.

Kwamishinoni da dama sun yi murabus a gwamnatin Fubara
Wike vs Fubara: Cikakkun Jerin Kwamishinonin da Suka Yi Murabus Zuwa Yanzu Hoto: Siminalayi Fubara, Nyesom Wike
Asali: Twitter

A safiyar ranar Alhamis, gwamnan ya sanya hannu a kasafin kudi, kuma kafin karshen ranar akalla kwamishinoni shida suka yi watsi da Fubara. Ga jerin kwamishinonin a kasa.

Kara karanta wannan

Rikicin Rivers: Jerin kwamishinoni 4 da suka ajiye aiki saboda Wike, suka juya wa Fubara baya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Cif Dr. Jacobson Nbina JP

Nbina ya kasance kwamishinan sufuri wanda ya mika takardar murabus din sa a ranar Juma’a.

Yayin da yake godewa gwamnan, Nbina ya bayyana dalili na kashin kai da matsalolin iyaye a matsayin dalilin murabus dinsa.

2. Gift Worlu

Worlu shine kwamishinan gidaje, wanda ya mika wasikar ajiye aiki ga Gwamna Fubara.

Yayin da yake alkawarin ci gaba da ba da goyon baya ga walwala da ci gaban al’ummar jihar, Worlu ya kuma bayyana dalili na kashin kai da ke bukatar kulawarsa cikin gaggawa.

3. Farfesa Zacchaeus Adangor

Adangor shine atoni janar kuma kwamishinan shari'a na jihar. Shine kwamishina na farko da ya mika takardar barin aiki ga Gwamna Fubara.

Farfesan wanda ya kuma yi aiki a matsayin atoni janar karkashin gwamnatin Wike, ya ce ya ajiye aikin ne saboda dalili nasa na kansa.

Kara karanta wannan

Karin bayani: Kwamishinoni huɗu sun yi murabus daga muƙamansu a jihar PDP, sun faɗi dalili

4. Dr Des George-Kelly

George-Kelly, wanda shi ne kwamishinan ayyuka a karkashin Gwamna Fubara, shi ma ya mika takardar murabus dinsa a ranar Alhamis.

Kamar yadda jaridar The Punch ta rahoto, tsohon kwamishinan ya bayyana cewa zuciyarsa ba zai bar shi ya ci gaba da aiki da gwamnan ba.

5. Emeka Woke

Woke shi ne kwamishinan ayyuka na musamman kuma yana daya daga cikin kwamishinoni na farko da suka mika takardar murabus dinsu.

Ya kasance shugaban ma'aikatan Wike na tsawon shekaru takwas a jere.

6. Misis Inime Aguma

An nada Aguma a matsayin kwamishinar jin dadi da walwala amma kuma ta mika takardar murabus dinta bayan rusa majalisar dokokin jihar.

A cikin wasikar murabus din ta, ta bayyana cewa tana da sauran ayyuka.

7. Isaac Kamalu

Kamalu, kwamishinan kudi na jihar shi ma ya bi sahun masu yin murabus wanda ya girgiza gwamnatin gwamna Fubara a ranar Alhamis.

Kara karanta wannan

Yanzu: Tinubu ya yi kokarin sulhu tsakanin Wike da Fubara, APC ta yi karin haske

Da yake mika godiyarsa ga gwamnan, bai bayar da wani dalili na yin murabus ba yayin da ya bayyana cewa zai fara aiki nan take.

8. Farfesa Chinedu Mmom

Mmom, kwamishinan ilimi na jihar, bai bayyana dalilinsa na yin murabus ba, sai dai ya yiwa gwamnan fatan alheri. Ya ce:

"Ina so in nuna godiya ta ga damar da aka ba ni na yin aiki a cikin gwamnatin ka tare da yi maka fatan alheri yayin da kake ci gaba da gudanar da mulkin jihar."

APC na zawarci ministan Abuja

A wani labarin, mun ji cewa APC mai rike da mulkin kasa ta kara kaimi wajen ganin ta dauke Nyesom Wike daga jam’iyyar hamayya watau PDP.

Labari ya zo daga Daily Trust cewa shugabannin jam’iyyar APC sun yi wa Nyesom Wike alkawarin shugabanci idan ya bar PDP.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng