Atiku da Ɗangote Sun Lale Naira 3bn Sun Baiwa Ɗan Takarar Gwamna a Arewa? Gaskiya Ta Yi Halinta

Atiku da Ɗangote Sun Lale Naira 3bn Sun Baiwa Ɗan Takarar Gwamna a Arewa? Gaskiya Ta Yi Halinta

  • Sanata Dino Melaye ya musanta jita-jitar cewa Atiku da Ɗangote sun ba shi N3bn kafin zaben gwamnan jihar Kogi
  • Melaye, ɗan takarar PDP a zaben da aka yi ranar 11 ga watan Nuwamba, ya ce rahoton kanzon kurege ne babu kanshin gaskiya
  • Ya kuma bayyana wasu darussa da a cewarsa ya koye su a lokacin zaɓen jihar Kogi da aka kammala

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kogi - Ɗan takarar gwamnan jihar Kogi a inuwar PDP a zaben da aka yi kwanan nan, Sanata Dino Melaye, ya yi bayani kan kuɗin da ake zargin ya karɓa.

Dino Melaye da Atiku Abubakar.
Zaben Kogi: Ban Karbi Naira Biliyan Uku Daga Hannun Atiku da Dangote Ba - Melaye Hoto: @Atiku
Asali: Twitter

Sanata Melaye ya musata raɗe-raɗin da ke yawo cewa ya samu makuɗan kuɗi har N3bn daga wurin tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da Aliko Ɗangote.

Kara karanta wannan

Kaduna: Gwamna Sani ya caccaki kalaman DHQ kan dalilin jefa bam a taron Musulmai, ya nemi abu 1

Ya bayyana haka ne a wurin wata liyafa da aka shirya domin girmama shi a birnin tarayya Abuja ranar Alhamis, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ɗan takarar wanda ya sha ƙasa, ya ce wasu bara gurbi masu neman kauda hankalin jama'a ne suka kirkiri wannan jita-jitar da nufin ɓata wa tawagar kamfe dinsa suna.

Da yake musanta zargin gaba ɗaya, Melaye ya byyana rade-radin cewa ya karbi N1bn daga Atiku da kuma N2bn daga Dangote a matsayin "labarin karya" da "maciya amana" suka ƙirƙira.

Na koyi darussa a zaben Kogi - Melaye

Tsohon dan majalisar tarayya ya kuma zayyana darussa guda uku da ya koya daga tsayawa takara a zaɓen Kogi da aka yi ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023.

Ya ce:

"Ɗaya daga cikin darussan da na koya shi ne, shiyyar gabas sun gane ba zasu iya kafa gwamna su kaɗai ba, dole sai sun haɗa kai sauran shiyyoyin kafin su cimma nasara."

Kara karanta wannan

"Ba ku ci bulus ba" Shugaba Tinubu ya ɗauki mataki mai tsauri kan sojojin da suka jefa bam a Kaduna

Dan takarar gwamnan na PDP ya kuma ƙara da cewa akwai bukatar hadin kai tsakanin mambobin PDP a jihar musamman a Kogi ta Yamma idan ana son jam'iyyar ta iya cin zaɓe.

Dalilin da ya sa gwamnan Ondo da zai yi murabus ba

A wani rahoton na daban Har yanzu ana ta takaddama kan yanayin rashin lafiyar Gwamna Rotimi Akeredolu na jihar Ondo.

Yayin da wasu ke ganin ya kamata ya yi murabus saboda rashin lafiya, Gwamnatin Ondo ta ce gwamna na yin aikinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel