Kano: ’Yan Sanda Sun Tura Gargadi Ga Jam’iyyun APC, NNPP Kan Shirin Zanga-Zanga a Jihar
- Jami’an ‘yan sanda a jihar Kano sun gargadi jam’iyyun APC da NNPP kan shirinsu na yin zanga-zanga a ranar Asabar
- Rundunar ta ce ba ta samu wata takarda dangane da zanga-zangar ba inda ta gargadi jama’a da su guji ta da zaune tsaye
- Kakakin rundunar, Abdullahi Kiyawa shi ya bayyana haka a yau Juma’a 24 ga watan Nuwamba a Kano
Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Kano – Rundunar ‘yan sanda jihar Kano ta gargadi masu zanga-zanga kan hukuncin kotun daukaka kara da aka yi a makon jiya.
Rundunar ta tura gargadin ne ga jam’iyyun NNPP da APC yayin da su ka shirya zanga-zanga a ranar Asabar 25 ga watan Nuwamba.

Asali: Facebook
Yaushe za a yi zanga-zanga a Kano?
Jam’ian ‘yan sanda sun ce za su yi maganin duk wani wanda ke son ta da zaune tsaye yayin zanga-zangar a Kano, Tribune ta tattaro.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Har ila yau, rundunar ta umarci dukkan jam’iyyun da su watsar da wannan shiri da su ke yi na zanga-zangar.
Idan ba a mantaba, jam’iyyun APC da NNPP sun bukaci magoya bayansu su fito don yin zanga-zanga kan hukuncin kotu mai sarkakiya.
Martanin 'yan sanda kan zanga-zangar a Kano
Kakakin rundunar a jihar, Abdullahi Kiyawa a madadin kwamishinan ‘yan sanda shi ya bayyana haka a yau Juma’a 24 ga watan Nuwamba a Kano.
Ya ce:
“Mun samu bayanai cewa jam’iyyun APC da NNPP na neman hadin kan magoya bayansu don gudanar da zanga-zanga a Kano.
“Mn kuma samu bayanan sirri cewa masu zanga-zangar sun shirya kai hari gidajen wadanda ba sa tare da su wanda hakan zai kawo rudani.

Kara karanta wannan
Kano: Abba Kabir, APC sun ja layi kan zanga-zangar da aka gudanar bayan fitar da takardun CTC
“Don haka runduarmu ba ta samu takarda kan haka ba, kuma duk wanda ya yi zanga-zangar da za ta ta da hankulan jama’a za mu yi maganinshi.”
Kiyawa har ila yau, ya shawarci masu zanga-zangar da su yi ta karkashin doka ba tare da saba duk wani tsari na hukuma ba, cewar Tori News.
APC, NNPP sun shirya yin zanga-zanga a Kano
Kun ji cewa, jam’iyyun APC da NNPP sun shirya gudanar da zanga-zanga a gobe Asabar 25 ga watan Nuwamba.
Wannan na zuwa ne bayan yanke hukuncin kotun daukaka kara a makon da ya gabata.
Asali: Legit.ng