Daga Karshe Kotun Daukaka Kara Ta Fitar da Muhimman Takardu Kan Hukuncin Shari'ar Gwamnan Kano

Daga Karshe Kotun Daukaka Kara Ta Fitar da Muhimman Takardu Kan Hukuncin Shari'ar Gwamnan Kano

  • Kotun ɗaukaka ƙara ta fitar da takardun hukuncin shari'ar zaɓen gwamnan Kano da ta yanke a ranar Juma'a, 17 ga watan Nuwamba
  • Salihu Tanko Yakasai da Abdulaziz Na'ibi Abubakar su ne suka sanya takardun na CTC a shafukansu na X
  • Fitar da takardun dai na zuwa ne bayan jam'iyyar NNPP ta koka kan cewa kotun ɗaukaka ƙarar ta ƙi fitar da takardun

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kano - Kwanaki biyar bayan yanke hukunci, kotun daukaka ƙara ta saki takardun hukuncin shari'ar gwamnan Kano da ta yanke.

Kotun ɗaukaka ƙarar ta yanke hukuncin ne a kan zaɓen gwamnan jihar Kano da ake takaddama a kai a ranar Juma'a, 17 ga watan Nuwamba, inda ta ba jam'iyyar APC da ɗan takararta, Nasiru Gawuna, nasara.

Kara karanta wannan

Jam'iyyar PDP ta bayyana hanyar da za ta bi domin kwato kujerar gwamnan APC a Arewa

Kotu ta saki takardun hukuncin shari'ar gwamnan Kano
Kotun daukaka kara ta fitar da takardun hukuncin shari'ar gwamnan Kano Hoto: Nasiru Yusuf Gawuna, Abba Kabir Yusuf
Asali: Facebook

Salihu Tanko Yakasai, wanda aka fi sani da Dawisu, ɗan takarar gwamnan jihar Kano a ƙarƙashin jam'iyyar PRP a zaɓen 2023 ne ya sanya takardun na CTC a shafinsa na X (wanda a baya aka fi sani da Twitter).

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A halin yanzu Dawisu jigo ne a jam’iyyar APC kuma na hannun daman Abdullahi Umar Ganduje, shugaban jam’iyyar APC na ƙasa.

Kotun ɗaukaka ƙara ta fitar da takardun CTC

Ya rubuta a yammacin ranar Talata, 21 ga Nuwamba, tare da takardun na CTC cewa:

"Kotun ɗaukaka ƙara ta bambanta ƙararrakin biyu; Peter Obi da na Kano APC da NNPP. Shafuffuka na 64 zuwa 67 sun yi bayani tare da hujjoji don tabbatarwa. Kasancewar mamba a jam'iyya na iya zama al'amarin gabanin zaɓe da kuma na bayan zaɓe. Ina fatan wannan zai sa wannan ya kawo ƙarshen taƙaddamar."

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ne ya sa kotu ta tsige Abba Gida-Gida da gwamnonin PDP 2? Gaskiya ta fito daga Villa

Abdul-Aziz Na'ibi Abubakar, jigo a jam'iyyar PDP, shi ma ya sanya takardun na CTC a shafinsa na X.

Sakin takardun na CTC na zuwa ne kwana guda bayan da muƙaddashin shugaban jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) na ƙasa, Abba Kawu Ali, ya koka kan gazawar kotun ɗaukaka ƙara na sakin takardun CTC na shari’ar Kano.

Ali ya yi zargin cewa akwai ƙoƙarin da ake yi da gangan domin kawo wa NNPP cikas.

Obasanjo Ya Magantu Kan Tsige Gwamnoni

A wani labarin kuma, tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo, ya yi magana kan yadda kotu na ke tsige gwamnoni a ƙasar nan.

Obasanjo ya yi nuni da cewa bai kamata alƙalai uku kacal su sauya zaɓin da miliyoyin ƴan Najeriya suka yi a lokacin zaɓe ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng