Hukuncin Kotun Koli: Ganduje Ya Bayyana Shekarar da Atiku, Peter Obi Za Su Yi Takarar Shugaban Kasa

Hukuncin Kotun Koli: Ganduje Ya Bayyana Shekarar da Atiku, Peter Obi Za Su Yi Takarar Shugaban Kasa

  • A ranar Alhamis, 26 ga watan Oktoba ne kotun koli ta yi fatali da shari'ar Peter Obi da Atiku kan Bola Tinubu saboda rashin hujjoji
  • Babbar kotun ta kuma ayyana Tinubu a matsayin ainahin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na 2023
  • Bayan hukuncin da kotu ta yanke, shugaban APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya bukaci abokan hamayyar Tinubu da su jira 2031 don takarar kujerar shugaban kasa

FCT, Abuja - Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya bukaci dan takarar PDP, Atiku Abubakar da takwaransa na LP, Peter Obi da su jira zuwa 2031 domin cimma kudirinsu na son zama shugaban kasa Bayan cikar wa'adin mulkin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ba biyu.

Ganduje ya bukaci Atiku da Obi a kan su jira 2031 don sake takara
Hukuncin Kotun Koli: Ganduje Ya Bayyana Shekarar da Atiku da Peter Obi Su Yi Takarar Shugaban Kasa Hoto: Mr. Peter Obi, Dr. Abdullahi Umar Ganduje OFR, Atiku Abubakar
Asali: Facebook

Tsohon gwamnan na jihar Kano ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis, 26 ga watan Oktoba, yayin da yake jinjinawa hukuncin kotun koli wanda ya tabbatar da nasarar Tinubu a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu.

Kara karanta wannan

Jiga-jigan PDP 4 da Su ka Nuna Farin Ciki da Nasarar Tinubu Kan Atiku a Kotun Koli

Ganduje ya bayyana a cikin wata sanarwa daga hadiminsa, Edwin Olofu, cewa hukuncin ya kawo karshen dukkanin ikirarin da jam'iyyun adawa ke yi na cewa an yi magudi a zaben shugaban kasar don Tinubu ya yi nasara, jaridar Punch ta rahoto.

Ya bayyana cewa sakamakon hukuncin kotun kolin zai bayar da damar da Tinubu zai mayar da hankalinsa kan muhimmin aikin kasa, Channels TV ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jiga-jigan siyasa sun cika da murna

Idan da rai da lafiya kuma aka cigaba da tafiya a haka, Bola Ahmed Tinubu ne shugaban Najeriya akalla har zuwa Mayun 2027.

Mun dai ji cewa magoya baya da shugabannin APC har da Muhammadu Buhari sun yi maraba da sakamakon da alkalan kotun koli su ka yi a jiya.

Obi ba zai shugabanci Najeriya ba, Reno

A wani labarin, mun ji cewa mai sukar siyasa kuma mai sharhi kan al'amuran jama'a, Reno Omokri ya mayar da martani kan hukuncin da kotun koli ta yanke na tabbatar da nasarar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Kara karanta wannan

Shari’ar Zabe: “Ku Yi Hakuri Zuwa 2031”, Ganduje Ya Tura Muhimmin Sako Ga Atiku, Obi

Omokri ya ce dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar LP, Peter Obi ba zai taba zama shugaban kasar Najeriya ba.

Ya bayyana wannan ne jim kadan bayan kotun koli ta yanke hukuncinta na karshe kan zaben shugaban kasa na 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Online view pixel