Jerin Jiga-Jigan PDP Da Shugaban Kasa Bola Tinubu Ya Bai Mukami

Jerin Jiga-Jigan PDP Da Shugaban Kasa Bola Tinubu Ya Bai Mukami

Jim kadan bayan nasarar Shugaban Kasa Bola Tinubu a babban zaben 2023, ana ta rade-radin cewa yana shirin kafa gwamnati ta hadin kan kasa ta hanyar nada wasu yan siyasa masu adawa mukamai.

Daga baya shugaban kasar ya ce ya fi sha'awar kafa gwamnati da za ta yi aiki don gina kasar.

Shugaban kasa Tinubu ya nada yan adawa a gwamnatinsa
Jerin Jiga-Jigan PDP Da Shugaban Kasa Bola Tinubu Ya Bai Mukami Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Sai dai kuma, yanayin mutanen da shugaban kasar ya ba mukamai tun bayan rantsar da shi ya tabbatar da rade-radin da aka dunga yi a baya.

Ya fara da nada Nyesom Wike, tsohon gwamnan jihar Ribas, a matsayin ministan Abuja, Shugaban kasa Tinubu ya nada wasu mambobin jam'iyyar adawa ta eoples Democratic Party (PDP) a gwamnatinsa.

Ga jerin sunayen wasu daga cikinsu:

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kara karanta wannan

Dalilin Da Yasa Na Yi Mamaki Da Tinubu Ya Nada Ni Ministan Abuja, Wike

1. Nyesom Wike - Ministan Abuja

Wike, wanda ya ki goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, a zaben 2023 saboda rikicin cikin gida, ya yarda cewa ya yi wa Tinubu aiki.

Harma an yi masa takwici da mukamin minista.

2. Chiedu Ebie - shugaban NDDC

A kwanan nan ne shugaban kasa Tinubu ya nada sabon kwamitin gudanarwa na hukumar raya yankin Neja Delta (NDDC).

Kamar yadda jaridar PM News ta rahoto, shugaban kwamitin, Chiedu Ebie mamba ne a jam'iyyar PDP a lokacin da aka sanar da nadin nasa.

An rahoto cewa tsohon Gwamna James Ibori wanda ya kasance aminin shugaban kasa Tinubu ne ya taimaka wa Ebie wajen samun mukamin.

3. Monday Igbuya, wakilin Delta a kwamitin NDDC

Rahotanni sun kuma kawo cewa wakilin jihar Delta a kwamitin NDDC, Monday Igbuya, ma dan PDP ne.

Kara karanta wannan

Ministan Abuja: Tsohon Gwamnan PDP Ya Fayyace Gaskiyar Wanda Yake Wa Aiki Tsakanin Tinubu da APC

Ana kuma zargin cewa Ibori ne ya taimaka wajen nadin nasa.

4. Victor Kolade Akinjo, wakilin Ondo, a kwamitin NDDC

Wakilin jihar Delta a kwamitin NDDC,Victor Kolade Akinjo, shima dan PDP ne.

Akinjo, tdohon dan majalisar wakilai kuma dan PDP ya sha kaye a kokarinsa na komawa majalisa a karo na uku inda dan takarar APC ya yi nasara.

5. Boma Iyaye, NDDC

Shugaban kasa Tinubu ya nada Boma Iyaye, dan PDP a jihar Ribas, a matsayin babban daraktan harkokin kudi na NDDC.

Bomo ya kasance akawu kuma tsohon kwamishinan wasanni a karkashin tsohon Gwamna Wike, ministan Abuja mai ci.

Na yi mamakin nada ni ministan Abuja, Wike

A wani labarin, mun ji cewa Nyesom Wike, ministan babban birnin tarayya Abuja, ya bayyana cewa nadinsa ba abu ne da ya sa rai ba.

Da yake jawabi a wata hira da Channels TV a ranar Laraba, 30 ga watan Agusta, tsohon gwamnan na jihar Ribas ya bayyana cewa ya yi mamaki lokacin da ya samu labarin nadin nasa a matsayin ministan Abuja.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng