Bayani Kan Ministocin Da Tinubu Ya Bada Sunayensu Da Shiyyoyin Da Suka Fito

Bayani Kan Ministocin Da Tinubu Ya Bada Sunayensu Da Shiyyoyin Da Suka Fito

  • Jerin sunayen mutanen da Tinubu ya fitar na baya-bayan nan ya gwada cewa Tinubu na mayar da alkhairi ga wanda ya hidimta ma sa
  • Za a iya tabbatar da hakan idan aka yi la'akari da yadda Tinubu ya yi rabon mukamansa a bangarori daban-daban na kasar nan
  • Shiyyar Arewa maso Yamma, wacce ta fi kowace bai wa Tinubu kuri'u, ita ce ta fi kowace shiyya samun yawan ministoci

FCT, Abuja - Shugaban kasa Bola Tinubu ya mika sunayen rukuni na biyu na ministocinsa ga Majalisar Dattawa domin tantancewa da tabbatarwa.

A kashi na biyu na jerin sunayen ministoci, Shugaba Tinubu ya gabatar da sunayen mutane 19, wanda yanzu yawansu gaba daya ya kai 47.

Shiyyoyin da ministocin Tinubu suka fito
Yawan kuri'un da kowace shiyya ta bai wa Tinubu da kuma yawan ministocin da suka samu. Hoto: Ahmed Bola Tinubu
Asali: Twitter

Mutanen da jerin sunayen ministocin na Tinubu ya kunsa

Jerin sunayen da aka fitar ya kunshi tsofaffin gwamnoni, masana, ‘yan majalisu da wasu fitattun ‘yan siyasa.

Kara karanta wannan

Abin da Shugaba Tinubu Ya Fada Mana a Aso Villa Inji Shugabannin ‘Yan Kwadago

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai kuma bincike ya nuna cewa shugaban kasar ya nada ministoci daga wasu shiyyoyin bisa la’akari da yawan kuri’un da suka ba shi.

A zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu, yankin Arewa maso Yamma ya bai wa jam’iyyar APC da dan takararta, Bola Tinubu kuri’u mafi yawa, wanda hakan ya ba shi nasarar lashe zabe.

Wani bincike na jaridar The Cable, ya nuna cewa Shugaba Tinubu ya samu kashi 30% na kuri’unsa ne daga yankin Arewa maso Yamma, yayin da yankin Kudu maso Gabas ya bashi mafi karancin kuri’u.

Tinubu ya sakawa wadanda suka hidimta ma sa da mukaman ministoci

Da yake tsokaci kan jerin sunayen, MS Ingawa, wani mai sharhi kan al'amuran jama'a, ya ce an san Bola Ahmed Tinubu da iya gano hazikan mutane da kuma sakawa wadanda suka hidimta ma sa.

Kara karanta wannan

APC: Adamu Ya Yi Murabus Ne Bayan Ya Gano Kotu Ta Rushe Zaben Tinubu? Gaskiya Ta Bayyana

Ga bayanin yadda kowane yanki ya zabi shugaba Tinubu a zaben 2023 da ya gabata, da kuma adadin ministocin da suka samu.

ShiyyaYawan kuri'uKaso cikin 100Ministoci
Arewa maso Yamma2,652,23530%10
Kudu maso Yamma2,542,97925.9%9
Arewa ta Tsakiya1,760.99320%8
Arewa maso Gabas933,17613.5%8
Kudu maso Kudu799,9579.1%7
Kudu maso Gabas127,6051.5%5

Jihohin da Shugaba Tinubu ya bai wa ministoci guda 2

Legit.ng a baya ta kawo rahoto kan sunayen mutanen da Shugaba Bola Tinubu ya zabo a matsayin wadanda zai bai wa ministoci.

Akalla ko wace jiha daga cikin jihohi 36 ciki har da FCT da muke da su, ta samu mutum daya da za a nada a matsayin minista. Sai dai akwai jihohin da suka yi sa'ar samun mutane biyu cikin wadanda za a bai wa mukamin ministoci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng