Labari Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Nada Atiku, Lalong, Matawalle a Karin Ministoci 19
- ‘Yan Majalisar Dattawa za su cigaba da tantance ragowar wanda ake so su zama Ministoci a kasar nan
- Bola Tinubu ya aiko sunayen wadanda ya zaba, a ciki akwai wasu tsofaffin Gwamnonin jihohi biyar
- A cikin wadanda aka zaba akwai Farfesa ahir Mamman OON, SAN da Sanata Aliyu Sabi Abdullahi
DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!
Abuja - Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya karanto karin Ministocin da ake sa ran za a nada bayan an tantance su.
Channels TV ta kawo rahoto cewa akwai tsofaffin Gwamnonin jihohin APC a cikin jerin.
Daga ciki akwai Gboyega Oyetola (Osun), Simon Lalong (Filato), Bello Matawalle (Zamfara) da Atiku Abubakar Bagudu (Kebbi).
![Shugaban Majalisar Dattawa Ministoci Shugaban Majalisar Dattawa Ministoci](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/95c6f2c6a2a916d1.jpg?imwidth=900)
Asali: Facebook
Har ila yau akwai Ibrahim Geidam wanda ya yi Gwamnan Yobe daga shekarar 2010 bayan rasuwar Mamman Ali har zuwa 2019.
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/e8472693d6fbdaed.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
Shugaba Tinubu Ya Fara Shawo Kan Shugabannin Kwadago a Taron Villa, Bayanai Sun Fito
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
Kamar yadda Daily Trust ta ce, akwai mutane 19 a cikin sahu na biyu na ragowar zababbun mutanen da za a tantance a majalisa.
A jerin akwai Ahmed Tijani, Dr Isiaka Salako, Dr Tunji Alausa da Tanko Sunisi da kuma jagorar mata a APC, Dr. Maryam Shetti.
Har ila yau, za a tantance Lola Ade John, Abubbakar Audu, Sabi Abdullahi, Alkali Samani a cikin wadanda za su rike mukaman.
A sunayen da aka gabatar a yauakwai matashin ‘dan kasuwan nan, Olatunbosun Tijani da tsohon ‘dan majalisa, Tanko Sununu.
Akwai fitaccen likitan koda, Dr. Tunji Alausa a jerin sababbin Ministocin da za su shiga ofis idan sun samu tantacewar majalisa.
Sanata Saidu Alkali Ahmed da Sanata Aliyu Sabi su na cikin wadanda za a tantance,
Cikakken jerin Ministocin
Wani daga cikin magoya bayan jam'iyyar APC mai-mulki, Malam Imran Muhammad ya tattaro sunayen a shafinsa na Twitter dazu.
- AHMED TIJJANI
- BOSUN TIJJANI
- DR MARYAM SHETTI
- ISHAK SALAKO
- TUNJI ALAUSA
- TANKO SUNUNU
- ADEGBOYEGA OYETOLA
- ATIKU BAGUDU
- BELLO MATAWALLE
- IBRAHIM GEIDAM
- SIMON BAKO LALONG
- LOLA ADEJO
- SHUAIBU ABUBAKAR
- TAHIR MAMMAN
- ALIYU SABI
- ALKALI AHMED
- HEINEKEN LOKPOBIRI
- UBA MAIGARI
- ZEPHANIAH JISSALO
Asali: Legit.ng