Ganduje Ya Kara Samun Gagarumin Goyon Baya Na Zama Shugaban APC Ta Kasa

Ganduje Ya Kara Samun Gagarumin Goyon Baya Na Zama Shugaban APC Ta Kasa

  • Tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje na ci gaba da samun karɓuwa a matsayin wanda zai gaji shugaban APC
  • Dattawan APC na Arewa ta Tsakiya sun ayyana goyon bayansu ga Ganduje ya zama muƙaddashin shugaban APC
  • A cewarsu, sun amince tsohon gwamnan ya maye gurbin Adamu amma bisa sharaɗin na riƙon kwarya ƙafin babban taro

Janar Lawrence Onoja, taohon hadimin tsohon shugaban ƙasa a mulkin soja, Marigayi Sani Abacha da wasu dattawan APC a Arewa ta Tsakiya, sun bayyana wanda suke bayan ya zama shugaban APC.

Jaridar Punch ta rahoto cewa jiga-jigan sun goyi bayan tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya maye gurbin tsohon shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Adamu.

Dakta Abdullahi Umar Ganduje, tsohon gwamnan jihar Kano.
Ganduje Ya Kara Samun Gagarumin Goyon Baya Na Zama Shugaban APC Ta Kasa Hoto: Punchng
Asali: Twitter

Sai dai dattawan APC na shiyyar sun kafa sharaɗin cewa sun aminta Ganduje ya maye gurbin Adamu amma a matsayin mukaddashi shugaban jam'iyya har sai an gudanar da babban taron kasa, Vanguard ta rahoto.

Kara karanta wannan

Bayan Tsawon Lokaci, An Bayyana Sunan Sabon Shugaban Jam'iyyar APC a Jihar Arewa

Yadda Ganduje ya samu karbuwa a shiyyoyin arewa

Wannan na zuwa ne kwana uku kacal bayan shugabannin APC na jihohi 7 a shiyyar Arewa maso Yamma, sun ayyana goyon bayansu ga Ganduje a wani taro da suka gudanar a Kaduna.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Haka zalika gamayyar jagororin Arewa ta tsakiya, ranar Alhamis, sun tabbatar da goyon bayansu ga tsohon gwamnan ya karɓi ragamar APC ta ƙasa.

Matakin shugaban ƙasa Bola Tinubu da gwamnonin APC na zaɓen Ganduje a matsayin wanda suke son ya gaji shugaban APC ya haifar da ruɗani da kace-nace tsakanin mambobi.

Yayin da wasu ƙusoshi ke ganin ya kamata a bar wanda zai maye gurbin Adamu ya fito daga jihar Nasarawa bisa tsarin raba muƙaman APC, wasu kuma sun goyi bayan zabin tsohon gwamnan Kano.

Muna goyon bayan Ganduje a matsayin shugaban riƙo - Dattawa

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Sanatan APC Na Shirin Murabus Daga Majalisar Dattawa, Sahihan Bayanai Sun Fito

Da yake jawabi ga yan jarida a Abuja, shugaban wakilan dattawan APC na Arewa ta tsakiya, Mista Onoja ya ce:

"Bamu yi mamaki ba don gwamnonin APC sun mara wa Ganduje baya da kuma wasu ƙungiyoyi da suka fito suka goyi bayan ya karɓi shugabancin jam'iyya na riko."
"Mu a matsayin wakilan dattawan jam'iyya na Arewa ta tsakiya, mun bi sahu wajen goyon bayan Abdullahi Ganduje. Muna goyon bayan ya ɗora daga inda Abdullahi Adamu ya tsaya."

Jam'iyyar APC Ta Sanya Ranakun Gudanar da Manyan Taruka Guda 2

A wani rahoton kuma Jam'iyyar APC mai mulki ta sanya ranar taron masu ruwa da tsaki da taron majalisar zartarwa (NEC) ta ƙasa.

Mukaddashin sakataren APC na ƙasa, Mista Festus Fuater, ya sanar da cewa tarukan biyu zasu gudana a ranakun 2 da 3 ga watan Agusta, 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262