Gwamna Aliyu Ya Aika Sunayen Kwamishinoni Ga Majalisar Dokokin Sokoto

Gwamna Aliyu Ya Aika Sunayen Kwamishinoni Ga Majalisar Dokokin Sokoto

  • Gwamna Ahmed Aliyu ya tura sunayen kwamishinoni 16 zuwa majalisar dokokin jihar Sakkwato ranar Alhamis
  • Ya ce wannan shi ne rukuni na farko kuma ya bi duk matakan da ya dace wajen zaɓo mutanen da ya naɗa
  • Shugaban majalisar ya sanar cewa zasu tantance mutanen a ranakun 2 da 3 ga watan Agusta, 2023

Sokoto state - Gwamna Ahmed Aliyu na jihar Sakkwato ya mika sunayen kwamishinoni 16 ga majalisar dokokin jihar, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito.

Sunayen wadanda gwamnan ya naɗa na kunshe ne a cikin wata wasika da ya aike wa shugaban majalisar, Alhaji Tukur Bala, kuma ya karanta wa mambobi a zauren majalisar ranar Alhamis.

Gwamna Ahmad Aliyu na jihar Sakkwato.
Gwamna Aliyu Ya Aika Sunayen Kwamishinoni Ga Majalisar Dokokin Sokoto Hoto: Ahmad Aliyu
Asali: Facebook

Gwamnan ya ambaci tanadin sashe na 192 da sauran sassan da suka dace na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na 1999 da aka yi wa kwaskwarima kan nadin kwamishinoni.

Kara karanta wannan

Gwamna Uba Sani Ya Sadaukar Da Kashi 50 Na Albashinsa Don Hidimtawa Talakawan Kaduna

Ya ce nadin mutanen 16 ya biyo bayan tuntuba da kuma bin matakan da suka dace kamar yadda yake kunshe a cikin dokokin aikin gwamnati.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

A rahoton Ripples, Gwamna Aliyu ya ce:

“Wannan naɗin kwamishinoni 16 shi ne rukunin farko kuma ya biyo bayan bukatar kafa majalisar zartarwa ta jiha kamar yadda yake ƙunshe a dokokin aikin gwamnati."

Majalisa ta sanya ranakun tantance sabbin kwamishinonin

Shugaban majalisar ya sanar da sauran mambobi cewa majalisar gaba daya za ta yi aikin tantance waɗanda aka zaba a ranakun 2 da 3 ga watan Agusta, 2023.

Jerin sunayen mutanen da gwamna Aliyu ya aika wa majalisa

Legit.ng Hausa ta tattaro muku jerin sunayen sabbin kwamishinonin da gwamna Aliyu ya aika zuwa majalisar dokoki, ga su kamar haka:

1. Tukur Alkali

2. Bala Kokani

Kara karanta wannan

Kace-Nace Yayin Da 'Yan Najeriya Suka Soki Yadda Tinubu Ya Zabi Ministoci, Sun Bayyana Abin Da Ya Kamata

3. Aminu Abdullahi

4. Mohammed Shagari

5. Nasiru Aliyu

6. Ya’u Danda

7. Yusuf Maccido.

8. Jamilu Gosta

9. Bashar Umar

10. Dakta Jabir Mai-Hulla

11. Balarabe Kadadi

12. Isa Tambagarka

13. Aliyu Tureta

14. Hadiza Shagari

15. Asabe Balarabe

16. Bello Wamakko.

Bayan Tsawon Lokaci, An Bayyana Sunan Sabon Shugaban Jam'iyyar APC

A wani labarin na daban kuma Barista Idris Shu'aibu ya samu nasarar zama sabon shugaban APC ta jihar Adamawa bayan taron kwamitin SEC.

Tsohon shugaban, Ibrahim Bilal ya rasa muƙaminsa ne kan zargin karkatar da kuɗaɗen jam'iyya a 2022.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262