Gwamna Zulum Ya Nada Tijani Bukar a Matsayin Sabon Sakataren Gwamnatin Jihar

Gwamna Zulum Ya Nada Tijani Bukar a Matsayin Sabon Sakataren Gwamnatin Jihar

  • Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya naɗa sabon sakataren gwamnatin jihar (SSG)
  • Gwamnan ya amince da naɗin Bukar Tijani a matsayin sabon SSG a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Isa Gusau ya fitar a ranar Laraba
  • Tijani ya taɓa riƙe muƙamin minista a gwamnatin tsohon shugaba Goodluck Jonathan kafin daga nan ya wuce majalisar ɗinkin duniya

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Borno, Maiduguri - Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya naɗa Bukar Tijani, tsohon ministan shugaba Goodluck Jonathan, a matsayin sakataren gwamnatin jihar.

Jaridar Punch ta rahoto cewa mai magana da yawun gwamnan, Isa Gusau, shine ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, 12 ga watan Yuli.

Gwamna Zulum ya nada sabon SSG
Bukar Tijani ya taba rike mukamin ministan noma Hoto: The Governor of Borno State and @SadeeqKurbe
Asali: UGC

Tijani, wanda tsohon ƙaramin ministan noma ne da raya karkara, ya taɓa riƙe muƙamin mataimakin Sakataren majalisar ɗinkin duniya/mataimakin babban darektan hukumar noma da abinci.

Kara karanta wannan

"Ku Cire Tsoro" Gwamnan Arewa Ya Yi Karin Haske Kan Matakai 2 da Zai Ɗauka Kan Malamai 7,000 A Jiharsa

Sanarwar ta tabbatar da cewa gwamna Zulum ya naɗa Tijani matsayin sakataren gwamnatin jihar ne bayan ya gamsu da ƙwarewar da yake da ita.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Tarihin Tijani

A cewar rahoton Vanguard, an haifi Tijani mai shekara 62 a duniya a ƙauyen Damasak cikin ƙaramar hukumar Dikwa ta jihar Borno.

Ya yi karatun Firamarensa a makarantar Firamaren Monguno daga shekarar 1967 zuwa 1970 da makarantar Firamare ta Gubio daga shekarar 1970 zuwa 1973. Sannan ya yi karatun Sakandire a makarantar Sakandiren gwamnati ta Maiduguri daga shekarar 1973 zuwa 1978.

Ya yi digirinsa na farko a fannin kimiyyar tsirrai da ƙasa daga shekarar 1982 zuwa 1994 a kwalejin Tuskegee (wacce yanzu ta koma jami'ar Tuskegee) a birnin Alabama na ƙasar Amurka.

Tijani ya yi digirin digirgir a jami'ar Reading da ke UK a shekarar 1989.

Kara karanta wannan

To Fa: Gwamnan Arewa Ya Kori Ma'aikata da Dukkan Hadiman Da Magabacinsa Ya Naɗa Nan Take

Gwamna Zulum Ya Samar Da Motocin Kai Manoma Gonakinsu

A wani labarin na daban kuma, gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum, ya samar da motocin da za su riƙa jigilar manoma zuwa gonakinsu a jihar Borno.

Gwamnan ya sanar da samar da motoci 300 waɗanda za su yi jigilar manoman domin rage raɗaɗin cire tallafin man fetur da gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi a ƙasar nan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng