Gwamna Zulum Ya Nada Tijani Bukar a Matsayin Sabon Sakataren Gwamnatin Jihar
- Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya naɗa sabon sakataren gwamnatin jihar (SSG)
- Gwamnan ya amince da naɗin Bukar Tijani a matsayin sabon SSG a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Isa Gusau ya fitar a ranar Laraba
- Tijani ya taɓa riƙe muƙamin minista a gwamnatin tsohon shugaba Goodluck Jonathan kafin daga nan ya wuce majalisar ɗinkin duniya
DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!
Borno, Maiduguri - Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya naɗa Bukar Tijani, tsohon ministan shugaba Goodluck Jonathan, a matsayin sakataren gwamnatin jihar.
Jaridar Punch ta rahoto cewa mai magana da yawun gwamnan, Isa Gusau, shine ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, 12 ga watan Yuli.

Asali: UGC
Tijani, wanda tsohon ƙaramin ministan noma ne da raya karkara, ya taɓa riƙe muƙamin mataimakin Sakataren majalisar ɗinkin duniya/mataimakin babban darektan hukumar noma da abinci.

Kara karanta wannan
"Ku Cire Tsoro" Gwamnan Arewa Ya Yi Karin Haske Kan Matakai 2 da Zai Ɗauka Kan Malamai 7,000 A Jiharsa
Sanarwar ta tabbatar da cewa gwamna Zulum ya naɗa Tijani matsayin sakataren gwamnatin jihar ne bayan ya gamsu da ƙwarewar da yake da ita.
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
Tarihin Tijani
A cewar rahoton Vanguard, an haifi Tijani mai shekara 62 a duniya a ƙauyen Damasak cikin ƙaramar hukumar Dikwa ta jihar Borno.
Ya yi karatun Firamarensa a makarantar Firamaren Monguno daga shekarar 1967 zuwa 1970 da makarantar Firamare ta Gubio daga shekarar 1970 zuwa 1973. Sannan ya yi karatun Sakandire a makarantar Sakandiren gwamnati ta Maiduguri daga shekarar 1973 zuwa 1978.
Ya yi digirinsa na farko a fannin kimiyyar tsirrai da ƙasa daga shekarar 1982 zuwa 1994 a kwalejin Tuskegee (wacce yanzu ta koma jami'ar Tuskegee) a birnin Alabama na ƙasar Amurka.
Tijani ya yi digirin digirgir a jami'ar Reading da ke UK a shekarar 1989.

Kara karanta wannan
To Fa: Gwamnan Arewa Ya Kori Ma'aikata da Dukkan Hadiman Da Magabacinsa Ya Naɗa Nan Take
Gwamna Zulum Ya Samar Da Motocin Kai Manoma Gonakinsu
A wani labarin na daban kuma, gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum, ya samar da motocin da za su riƙa jigilar manoma zuwa gonakinsu a jihar Borno.
Gwamnan ya sanar da samar da motoci 300 waɗanda za su yi jigilar manoman domin rage raɗaɗin cire tallafin man fetur da gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi a ƙasar nan.
Asali: Legit.ng