'Dan Shugaba Obasanjo Ya Fadi Wadanda Suka Dace da Shugabancin Majalisar Tarayya

'Dan Shugaba Obasanjo Ya Fadi Wadanda Suka Dace da Shugabancin Majalisar Tarayya

  • Olujonwo Obasanjo ya na tallata takarar da Godswill Akpabio yake yi a majalisar dattawa na kasa
  • Yaron tsohon shugaban na Najeriya ya ce tsohon Gwamnan ya cancanci ya gaji Ahmad Lawan
  • A zaben majalisar wakilan tarayya, Olujonwo Obasanjo ya na tare da zabin APC, Tajudeen Abass

Abuja - Olujonwo Obasanjo wanda jagora ne a jam’iyyar APC, ya shiga cikin masu goyon bayan takarar Godswill Akpabio a majalisar dattawa.

Rahoton Premium Times ya nuna yaron tsohon shugaban na Najeriya ya goyi bayan Sanata Godswill Akpabio ya gaji kujerar Dr. Ahmad Lawan.

Haka zalika a zaben da za ayi a majalisar wakilan tarayya, Olujonwo Obasanjo ya na tare da Hon. Abbas Tajudeen wanda jam’iyyarsa ta ayyana.

'Yan takarar Majalisar Tarayya
Godswill Akpabio da Tajudeen Abbas Hoto: www.intelregion.com
Asali: UGC

Da yake zantawa da manema labarai a ranar Asabar da ta gabata, Obasanjo ya yi kira ga zababbun ‘yan majalisar tarayya su yi wa jam’iyya biyayya.

Kara karanta wannan

Zaben Majalisa: Tsohon Gwamnan Arewa Mai Yakar APC Ya Yi Kus-Kus da Kwankwaso

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

‘Dan siyasar ya ce Akpabio ya cancanci ya shugabanci ‘yan majalisar dattawa saboda irin biyayyar da ya nuna ga APC da zababben shugaban kasa.

Ana ganin girman Akpabio

"Akpabio ya saye fam din neman takarar shugaban kasa, amma a daren zaben tsaida gwani, sai ya janyewa zababben shugaban kasa, Bola Tinubu.
Shugabannin jam’iyyar APC, zababben shugaban Najeriya, da duka sauran masu ruwa da tsaki su na ganin girman Sanata Godswill Akpabio.

- Olujonwo Obasanjo

Saboda haka ana matukar maraba da ayyana shi a matsayin sabon shugaban majalisar dattawa.

Kamar yadda tsohon Gwamnan na Akwa Ibom ya cancanta, an rahoto Obasanjo yana cewa Abbas Tajudeen zai dace da shugaban majalisar wakilai.

Daga Gbaja sai Taju - Obasanjo

“Tajudeen Abass ya yi namijin kokari wajen bada gudumuwar kawo dokoki a majalisa, wannan kurum ya isa ya sa ya zama shugaban majalisa.

Kara karanta wannan

Shugaban Majalisa: Sababbin Sanatoci 18 Sun Botsarewa APC, An Fito da ‘Yan Takara Dabam

Wannan Basarake na kasar Zazzau ya yi zarra wajen harkar kawo dokoki, shi kadai ya kawo kudiri 74, a cikinsu shugaban kasa ya sa hannu a 21.

- Olujonwo Obasanjo

Akpabio ya yi karfi

An rahoto tsohon Gwamnan Akwa Ibom watau Godswill Akpabio ya ce Sanatoci kusan 70 ke goyon bayan shi, kuma za su iya kai 86 kafin zabe.

Godswill Akpabio ya ce ana amfani da kudi a zaben bana, ya ce Majalisar dattawa kunshe ta ke da masu daraja da ba za su bari a saida kasar ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng