Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana

Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana

'Rana bata karya'

Allah ya kawo mu ranar zaben shugaban kasar Najeriya 2023 inda yan Najeriya ke zaben wanda zai ja ragamar mulkin kasar daga 2023 zuwa 2027.

Yan takara 18 ne zasu fafata a wannan zabe kuma mutum milyan 87 da suka karbi katunan zabensu ake sa ran zasu fito ka'da kuria, bisa alkaluman INEC.

Sojoji da yan sanda sun isa makarantar firamare ta LEA, Lugbe

Sojoji da yan sanda sun isa makarantar firamare ta LEA da ke Lugbe, babban birnin tarayya don kwantar da tarzoman da ya barke tsakanin masu zabe da jami’an INEC.

An gano jami'an tsaron tsattsaye a wurare yayin da suka faka motarsu.

Jami'an tsaro rarrabe a gaban motarsu
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Original

Rikici ya kaure a makarantar Firamare ta LEA, Lugbe

Rikici ya kaure a rumfar zabe ta makarantar firamare ta LEA da ke Lugbe, babban birnin tarayya Abuja.

Masu zabe sun lakadawa jami’an INEC duka kan zarginsu da dangwala kuri’u da fadawa masu zabe cewa babu takardar zabe.

Jama'a na hatsaniya a wajen zabe
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Original

Abdulsalami ya sauke hakkinsa

Tsohon shugaban ƙasa a zamanin mulkin soja, Janar Abdulsalami Abubakar, tare da matarsa da iyalan gidansa sun kaɗa kuri'unsu a mazaɓarsu.

Abdulsalami Abubakar.
Abdulsalami Abubakar yayin da yake saka kuri'a a Akwatu Hoto: TVC
Asali: Twitter

Gwamna Ganduje ya kaɗa kuri'arsa

Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya kaɗa kuri'arsa a mazaɓar Ganduje, ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano.

Gwamnan Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.
Gwamna Ganduje ya saka kuri'a a Akwatun shugaban kasa.
Asali: Twitter

Jama’a sun fito zabe sosai a rumfar zabe na fadar shugaban kasa

Dandazon jama’a sun yi tururuwan fitowa a rumfar zabe ta PU 022 da ke fadar shugaban kasa domin aiwatar da yancinsu na yan kasa.

Masu zabe sun yi layi suna jiran ya kai kansu
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Original

Akwai matsala a jihar Kaduna, rumfuna da dama babu takardun zabe

Situation Room, gamayyar kungiyoyin fafutuka masu bibiyar zabe sun bayyana cewa akwai rumfuna da dama da har yanzu ba'a fara kada kuri'a ba.

A PU 02 da 03 dake unguwar Shanu, karamar hukumar Kaduna ta arewa, babu takardun zabe gaba daya.

Mai Martaba Sarkin Zazzau Ya Kada Kuri'arsa

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Bamalli, ya kada kuri'arsa a rumfar zaben dake wajen fadar Zazzau, rahoton Leadership.

Sarkin Zazzau
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana Hoto: Nat'aalah
Asali: Twitter

Jonathan da matarsa sun kaɗa kuri'a

Tsohon shugaban Najeriya, Dakta Goodluck Ebele Jonathan, tare da matarsa sun kaɗa kuri'unsu a Unit 39, Ward 13, Otuake, ƙaramar hukumar Ogbia a jihar Bayelsa.

Goodluck Jonathan.
Tsohon shugaban kasa, Jonathan lokacin da yake saka kuri'arsa a Akwatun zaɓe. Hoto: dailytrust
Asali: Twitter

Ministan sadarwa, Isa Pantami, ya kada kuri'arsa

Ministan sadarwar Najeriya kuma shehin malamin addinin Musulunci, Farfesa Isa Ibrahim Pantami, ya kada kuri'arsa yau Asabar.

Pantami wanda ya bayyana hakan a shafinsa na Tuwita ya yiwa Najeriya addu'a.

Yace:

"Allah ya taimaki kasarmu, Najeriya."

Pantami
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Twitter

Shugaban majalisar dattawa ya kada kuri’arsa

Shugaban majalisar dattawa, Lawan Ahmad ya bi sahun daukacin al’ummar Najeriya wajen kada kuri’arsa a mazabarsa da ke garin Gashua, jihar Yobe.

Shugaban majalisar dattawa ya kada kuri'arsa
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana Hoto: @DrAhmadLawan
Asali: Twitter

Osinbajo ya jefa kuri'a

Mataimakin shugaban ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya kaɗa kuri'arsa a mazabarsa da ke Unit 14, Ward 1, ƙaramar hukumar Ikenne, jihar Ogun.

Osinbajo, wanda ya isa wurin tare da mai ɗakinsa ya yaba da yadda zaben ke tafiya a jihar Ogun cikin kwanciyar hankali.

Jami’an zabe na wucin gadi sun yi zanga-zanga kan rashin biyansu alawus

Jami’an INEC na wucin gadi sun gudanar da zanga-zanga kan rashin biyansu alawus dinsu a yankin Dorayi, karamar hukumar Gwale da ke jihar Kano.

Ma’aikatan sun ayyana cewa ba za su yi aikin zabe ba idan har ba’a biyasu hakkinsu ba.

Kwankwaso ya kaɗa kuri'arsa

Tsohon gwamnan Kano kuma mai neman zama shugaban ƙasa a inuwar jam'iyar NNPP mai kayan marmari, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, ya kaɗa kuri'arsa.

Rabiu Musa Kwankwaso.
Kwankwaso ya kada kuri'a
Asali: Original

Mutane sun yi cirko-cirko a mazaba babu kayan zabe

Mutane sun yi cirko-cirko suna jiran tsammani, ba kayan zaɓe kuma babu jami'an hukumar zaɓe a rumfar Federal Low-Cost da ke gundumar Ɗan Iya Hardo, jihar Bauchi.

Mutane na jiran tsammani.
Mutane suna zaman jiran Malaman zaɓe a Bauchi
Asali: Original

Dattijuwa a Kwankwaso tace Allah ya bamu Shugaba Na Gari Albarkan Annabi Muhammadu (SAW)

Wata dattijuwa ta fito a garin Kwankwaso domin ka'da kuri'arta.

Dattijuwar mai suna Binta Yusuf ta bayyana Aminiya cewa Allah ya bamu shugaba Nagari.

Kalli bidiyon:

An fara zabe a yankin Matazu, jihar Katsina

An fara kada kuri’u a yankin karamar hukumar Matazu da ke jihar Katsina duk da cewar mutane yan kadan ne suka fito domin aiwatar da yancinsu na yan kasa.

Gwamna Nasir El-Rufai ya bi layi a rumfar zabensa

Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-rufai ya bi sahun sauran jama’ar mazabarsa wajen yin layi don kada kuri’a a rumfar zabensa da ke Ungwan Sarki, jihar Kaduna.

El-rufai na bin layi don kada kuri'arsa a rumfar zabensa ta Ungwan Sarki
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana Hoto: @GovKaduna
Asali: Twitter

Shugaba Muhammadu Buhari ya kada kuri'arsa

Shugaba Muhammadu Buhari tare da uwargidarsa, Aisha Muhammadu Buhari sun kada kuri'arsu a mazabarsu dake garin Daura, jihar Katsina.

Zaku tuna cewa Buhari ya tafi Daura ranar Juma'a tare da iyalinsa don zabe.

Buhari
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Twitter

Bola Tinubu ya isa rumfar zabensa

Ko'ina ya kaure da hayaniya yayin da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu ya isa mazabarsa. Jami'an tsaro sun mamaye koina yayin da Tinubu ke kokarin kada kuri'arsa.

Bola tinubu da matarsa a rumfar zabensa
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Original

Peter Obi ya isa rumfar zabensa

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi ya isa mazabarsa domin kada kuri’arsa a zaben da ke gudana a yau Asabar.

Yayin da yake zantawa da manema labarai a rumfar zabensa ta 019, Umudimakasi Square, Agulu, jihar Anambra, Obi ya nuna yakinin cewa shine zai yi nasara a zaben shugaban kasar.

Peter Obi yana jawabi ga manema labarai a rumfar zabensa
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana Hoto: @nigeriantribune
Asali: Twitter

An tsaurara tsaro a mazabar Kwankwaso

An ƙara tsaurara tsaron a mazaɓar dan takarar shugaban kasa a inuwar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso. Har zuwa karfe 10:08 tsohon gwamnan Kano bai isa rumfar zaben ba.

Mazabar Kwankwaso.
An kara girke jami'an tsaro a mazabar Kwankwaso.
Asali: Original

Diyar Tinubu ta isa rumfar zaben mahaifinta

Diyar Tinubu, Folashade Tinubu ta isa rumfar zaben mahaifinta kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu don kada kuri’arta.

Diyar Tinubu ta isa rumfar zaben mahaifinta
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Original

Okowa da matarsa sun dira rumfar zabe

Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam'iyyar PDP kuma gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa, tare mai ɗakinsa, Dame Edith Okowa, sun isa rumfar zaɓe Unit 14, Makarantar Firamaren Eghoma.

Jami’in INEC ya kwashi kayan zabe kan babur

A yankin Gadan Maiwa da ke karamar hukumar Ningi ta jihar Bauchi, an gano jami'in zabe kan hanyarsu ta tafiya wajen aikinsu dauke da wasu kayayyakin zabe a kan babur.

Jami'an zabe dauke da kayan zabe a kan babur
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana Hoto:@vanguardngrnews
Asali: Twitter

Matar Bola Tinubu ta kaɗa kuri'a

Mai dakin dan takarar shugaban kasa a inuwar jam'iyyar APC mai mulki, Oluremi Tinubu, ta kaɗa kuri'arta a Falomo, jihar Legas.

Atiku Abubakar Ya Dira Rumfar Zabensa Don Ka'da Kuri'arsa

Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Peoples Democratic Party PDP ya isa rumfar zabensa don kada kuri'arsa.

Tsohon mataimakin shugaban kasan ya ka'da kuri'arsa a mazabarsa dake Jimeta.

Atiku
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana Hoto: @MobilePunch
Asali: Twitter

Jami'an EFCC sun dira mazabar Tinubu

Jami'an hukumar yaki da rashawa ta EFCC sun dira rumfar zaben dan takarar shugaban kasa na APC, Asiwaju Bola Tinubu.

Tinubu
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Original

An fara kada kuri’a a mazabar Kwankwaso

An fara tantancewa tare da kada kuri’a a mazabar kwankwaso rumfar zabe ta 001.

Jami'in zabe yana tantance mai zabe
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Original

Mutane sun fara kada kuri'unsu
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana
Asali: Original

Mutane sun hau layi a rumfar zaɓen Kwankwaso

Tuni dai mutane suka hau layi a rumfar da ɗan takarar shugaban kasa na NNPP, Abiu Musa Kwankwaso, ke kaɗa kuri'a amma har yanzun ba'a manna sunayen mutane ba.

Jami'an hukumar zabe INEC da jami'an tsaro na wurin da misalin karfe 8:35 na safe.

Rumfar Kwankwaso
Mutane sun hau layi suna jiran a tantance su.
Asali: Original

Direbobi sun ki kai ma'akatan INEC wajen zabe saboda ba'a biyasu kudi ba

A birnin Ikeja jihar Legas, kawo karfe 8:30. direbobi sun ki kai ma'aikatan INEC rumfar zabensu.

Sun bayyana cewa sai an biyasu kudinsu zasu kai jami'an tare da kayan aiki.

Ikeja
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana Hoto: @Thecable
Asali: Twitter

An tsaurara matakan tsaro a mazabar Buhari da ke Daura

Jami’an INEC, ma’aikatan zabe na wucin gadi, jami’an ICPC, jami’an tsaro da sauransu suna nan a kasa a mazabar Shugaba Buhari da ke Daura yayin da ake shirin fara tantance masu zabe kamar yadda Channels Tv ta rahoto.

Jami'an tsaro jibge a mazabar Buhari da ke Daura
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana Hoto: @channelstv
Asali: Twitter

Masu zabe sun fara tururuwan fitowa a Ado-Ekiti

Mutane sun fara isa rumfunan zabensu don aiwatar da yancinsu na yan kasa a yankin Ado-Ekiti.

An gano masu zabe suna duba sunayensu a rumfar zabe ta Unit 9, Ward 11, Ado-Ekiti, jihar Ekiti.

Komai ya kankama a rumfar zaben Kwankwaso

Mutane sun fito rumfar zaben GGSS Kwankwaso, karamar hukumar Madobi inda dan takarar shugaban kasan jam'iyyar NNPP, Rabiu Kwankwaso zai kada kuri'arsa.

Madobi
Kai Tsaye: Jajibirin Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023 Hoto: @thecable
Asali: Twitter

Jami’an zabe sun fara shirya kayan zabe a mazabar Shugaba Buhari

Tun da misalin 7:57 na safe, jami’an zabe suka fara shirya wajen zabe a Baba Tone quarters da ke Waziri road, Sarkin Yara, Daura, jihar Kastsina.

Ana sa ran Shugaban kasa Muhammadu zai isa mazabar tasa da misalin karfe 9:30 domin ya kada kuri’arsa.

Jami'an zabe suna tsara wajen kada kuri'u
Kai Tsaye: Zaben Shugaban Kasar Najeriya 2023, Yadda Yake Gudana Hoto: @thecableng
Asali: Twitter

Jami'ai sun fara isa rumfunan zabe

Kayayyakin zaɓe sun isa rumfar da gwamnan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, ke kaɗa kuri'a watau PU OO4, gunduma ta 004, ƙaramar hukumar Ekiti ta yamma.

Online view pixel