‘Diyar Atiku ta Zama Lauyarsa, Ta Fadi Hikimar Gwanjon Kadarorin Najeriya a Kasuwa

‘Diyar Atiku ta Zama Lauyarsa, Ta Fadi Hikimar Gwanjon Kadarorin Najeriya a Kasuwa

  • Hauwa Atiku-Uwais ta goyi bayan a bude hannuwa a gayyato mutane domin bunkasa tattalin arziki
  • ‘Diyar Atiku Abubakar ta yarda da manufarsa ta yin gwanjo da wasu daga cikin kadarorin da ke Najeriya
  • Idan Atiku ya karbi shugabancin kasar nan a 2023, Hajiya Atiku-Uwais ta nuna ‘yan kasuwa za su ji dadi

Abuja - Hauwa Atiku-Uwais wanda diya ce ga Alhaji Atiku Abubakar, ta yabi manufar mahaifinta na jawo ‘yan kasuwa wajen kawo cigaban kasa.

A yayin da aka zanta da ita a tashar Channels TV, Hauwa Atiku-Uwais ta ce gwamnatin Atiku Abubakar za ta dage wajen kawo yarjejeniyar PPP.

‘Diyar ‘dan takaran shugaban kasar na jam’iyyar PDP ta ce tsarin hadin-gwiwar gwamnati da ‘yan kasuwa na PPP zai saukaka kasuwanci a Najeriya.

Atiku-Uwais ta ce mahaifinsu yana so ya bar tarihi mai kyau ne shiyasa yake neman shugabanci. Atiku ya neman takararsa ta shida kenan a 2023.

Kara karanta wannan

Saura kwana 5: Kungiyar Arewa ta AFC ta fadi dan takarar da take so ya gaji Buhari

Nasara ta na wajen Atiku a ranar Asabar

A tattaunawar da aka yi da ita Atiku-Uwais ta nuna sa ran Wazirin Adamawa zai lashe zabe.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Idan ‘dan takaran na jam’iyyar PDP ya yi nasarar zama shugaban kasa a Mayun 2023, ‘diyarsa ta ce gwamnatinsa za ta yi gwanjon kadarorin kasar.

‘Diyar Atiku
Atiku Abubakar a Abuja Hoto: @Atiku.org
Source: Facebook

Saida wadannan kadarori zai jawo a shiga yarjejeniyar PPP, wanda Atiku-Uwais ta ce hakan zai taimaki Najeriya domin zai zaburar da cigaba sosai.

Atiku-Uwais: Amfanin kawo kamfanoni

A kundin manufofinsa ga ‘Yan Najeriya, shi (Atiku) ya yi ta bayani a kan kawo masana’antu da kuma saida kadarorin gwamnati.
Idan ka bada dama ‘yan kasuwa suka shigo, za a samu kamfanoni da ke aiki, kamfanoni za su rika kawo kudi, ana biyan haraji.
Sannan gwamnati za ta samu damar yin harkokin gabanta, a kuma daina dogara kaco-kam da harkar mai.
A ra’ayina, bude hannuwa da saida kadarori za su yi sanadiyyar da kamfanoni za su shiga yarjejeniya da gwamnati.

Kara karanta wannan

2023: Jerin Sunayen Manyan Malaman Addini Da Ke Takara a Zabe Mai Zuwa

Wannan zai bada dama gwamnati ta maida hankali kan aikin gabanta na kawo dokoki da ganin an ji dadin kasuwanci.

- Hauwa Atiku-Uwais

Adadin wakilan zabe a 2023

Kun samu labari INEC ta ce PDP ce ta farko a yawan wakilan zabe sama da 176, 500, Jam’iyyar hamayyar ta na da 11.2% na kason duka wakilan 2023.

Kusan za a iya cewa jam'iyyar NNPP ta bada mamaki domin APC mai mulki ta tsere mata da mutane uku kacal ne a adadin sunayen wakilan zabe.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng