2023: Bola Tinubu Ya Ziyarci Gwamna Makinde Na PDP a Ibadan

2023: Bola Tinubu Ya Ziyarci Gwamna Makinde Na PDP a Ibadan

  • Tsohon gwamnan Legas kuma ɗan takarar shugaban kasa a APC, Bola Tinubu, ya ziyarci gwamna Makinde a Ibadan
  • Wannan ziyara na zuwa ne awanni 24 bayan Tinubu ya gana da gwamna Wike a gidan gwamnatin Ribas dake Patakwal
  • Makinde, mamaban G5, ya ce mutanen Oyo sun shirya tsaf su zabi wanda zai zama sanadin haɗin kan Najeriya

Oyo - Ɗan takarar shugaban ƙasa a inuwar All Progressives Congress, Asiwaju Bola Tinubu, ya ziyarci gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, a a gidan gwamnatinsa da ke Ibadan.

Jaridar Punch ta rahoto cewa Bola Tinubu tare da jiga-jigan jam'iyyar APC da mambobin tawagar PCC suna Ibadan domin halartar gangamin ralin kamfen shugaban kasa.

Tinubu da Makinde.
2023: Bola Tinubu Ya Ziyarci Gwamna Makinde Na PDP a Ibadan Hoto: Seyi Makinde
Asali: Facebook

Sai dai Legit.ng Hausa ta gano cewa APC ta tsara gudanar da ralin a makon da ya gabata ranar Talata amma daga baya ta sauya shawari ta dawo da shi yau Alhamis, 16 ga watan Fabrairu, 2023.

Kara karanta wannan

Atiku Ya Kara Shiga Tasku, Gwamnan PDP Ya Yanke Shawara Ta Karshe Ya Faɗi Wanda Yake Goyon Baya a 2023

Kwamitin kamfen Tinubu/Shettima ya sauya ranar Ralin ne sakamakon zanga-zangar da ta ɓarke daga fusatattun 'yan Najeriya kan karancin man Fetur da karancin takardun naira.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Wanda mutanen Oyo zasu zaɓa a 2023 - Makinde

Bayan ya karbi bakuncin tawagar, gwamna Makinde ya ce mutanen jiharsa ta Oyo a shirye suka su jefa kuri'unsu ga ɗan takarar da nasararsa zata nuna adalci, daidaito da haɗin kan Najeriya.

Ya ce gwamnatinsa ta yi amanna da sanya bukatun al'umma a matakin farko, inda ya ƙara da cewa, "Masu buga wasan siyasa zasu zo su tafi amma ƙasar mu Najeriya na nan."

Haka nan da yake karin haske kan matsayar tawagar G-5 da kuma rigingimun cikin gida a jam'iyyar PDP, Makinde ya ce:

"Idan muna da zaɓi biyu tsakanin burinmu na kashin kai da kuma haɗin kan ƙasa, zamu zaɓi dunkulewar Najeriya ne a farko."

Kara karanta wannan

An samu mafita: Ana tsaka da shan wahalar Naira, Buhari zai yiwa 'yan Najeriya jawabi

Ya ce G-5 ta bibiyi zaben fidda gwanin da ya samar da Tinubu a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa kuma ta yaba da matakin gwamnonin arewa, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

Gwamna Ortom Ya Yanke Shawara Kan wanda zai wa aiki a 2023

A wani labarin kuma Gwamna Ortom ya tabbatar da cewa yana tare da burin ɗan takarar shugaban kasa a inuwar LP, Peter Obi.

Gwamnan Benuwai, Samuel Ortom, mamban G-5, ya bukaci matasa su tashi tsaye su tasa Obi har zuwa kan kujera lamba ɗaya a zabe mai zuwa. A wurin wani taron magiya bayan Peter Obi da suka fi shahara da Obidient, Ortom ya baygana cikakken goyon bayansa ga tsohon gwamnan Anambra.

Asali: Legit.ng

Online view pixel