2023: Bola Tinubu Ya Ziyarci Gwamna Makinde Na PDP a Ibadan

2023: Bola Tinubu Ya Ziyarci Gwamna Makinde Na PDP a Ibadan

  • Tsohon gwamnan Legas kuma ɗan takarar shugaban kasa a APC, Bola Tinubu, ya ziyarci gwamna Makinde a Ibadan
  • Wannan ziyara na zuwa ne awanni 24 bayan Tinubu ya gana da gwamna Wike a gidan gwamnatin Ribas dake Patakwal
  • Makinde, mamaban G5, ya ce mutanen Oyo sun shirya tsaf su zabi wanda zai zama sanadin haɗin kan Najeriya

Oyo - Ɗan takarar shugaban ƙasa a inuwar All Progressives Congress, Asiwaju Bola Tinubu, ya ziyarci gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, a a gidan gwamnatinsa da ke Ibadan.

Jaridar Punch ta rahoto cewa Bola Tinubu tare da jiga-jigan jam'iyyar APC da mambobin tawagar PCC suna Ibadan domin halartar gangamin ralin kamfen shugaban kasa.

Tinubu da Makinde.
2023: Bola Tinubu Ya Ziyarci Gwamna Makinde Na PDP a Ibadan Hoto: Seyi Makinde
Asali: Facebook

Sai dai Legit.ng Hausa ta gano cewa APC ta tsara gudanar da ralin a makon da ya gabata ranar Talata amma daga baya ta sauya shawari ta dawo da shi yau Alhamis, 16 ga watan Fabrairu, 2023.

Kwamitin kamfen Tinubu/Shettima ya sauya ranar Ralin ne sakamakon zanga-zangar da ta ɓarke daga fusatattun 'yan Najeriya kan karancin man Fetur da karancin takardun naira.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Wanda mutanen Oyo zasu zaɓa a 2023 - Makinde

Bayan ya karbi bakuncin tawagar, gwamna Makinde ya ce mutanen jiharsa ta Oyo a shirye suka su jefa kuri'unsu ga ɗan takarar da nasararsa zata nuna adalci, daidaito da haɗin kan Najeriya.

Ya ce gwamnatinsa ta yi amanna da sanya bukatun al'umma a matakin farko, inda ya ƙara da cewa, "Masu buga wasan siyasa zasu zo su tafi amma ƙasar mu Najeriya na nan."

Haka nan da yake karin haske kan matsayar tawagar G-5 da kuma rigingimun cikin gida a jam'iyyar PDP, Makinde ya ce:

"Idan muna da zaɓi biyu tsakanin burinmu na kashin kai da kuma haɗin kan ƙasa, zamu zaɓi dunkulewar Najeriya ne a farko."

Ya ce G-5 ta bibiyi zaben fidda gwanin da ya samar da Tinubu a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa kuma ta yaba da matakin gwamnonin arewa, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

Gwamna Ortom Ya Yanke Shawara Kan wanda zai wa aiki a 2023

A wani labarin kuma Gwamna Ortom ya tabbatar da cewa yana tare da burin ɗan takarar shugaban kasa a inuwar LP, Peter Obi.

Gwamnan Benuwai, Samuel Ortom, mamban G-5, ya bukaci matasa su tashi tsaye su tasa Obi har zuwa kan kujera lamba ɗaya a zabe mai zuwa. A wurin wani taron magiya bayan Peter Obi da suka fi shahara da Obidient, Ortom ya baygana cikakken goyon bayansa ga tsohon gwamnan Anambra.

Asali: Legit.ng

Online view pixel