Surukin Buhari da Ya Sauya-Sheka Ya Fara Kamfe, Yana Kira a Guji APC a 2023
- Muhammad Sani Sha’aban ya fara yakin neman zama Gwamnan Kaduna a karkashin jam’iyyar ADP
- Hon. Sani Sha’aban ya kaddamar da kamfe a garin Tashar Yari, ya bukaci ‘Yan Kaduna su zabe shi a 2023
- ‘Dan siyasar ya yi alkawarin samar da tsaro, ya ce ba zai ci amanar jama’a idan ya shiga gidan gwamnati ba
Kaduna - Muhammad Sani Sha’aban wanda suruki ne a wajen Muhammadu Buhari ya soma yakin neman zama Gwamnan jihar Kaduna a zabe.
Hon. Muhammad Sani Sha’aban yana takarar Gwamnan Kaduna a karkashin jam’iyyar adawa ta ADP, biyo bayan sauya-shekarsa daga APC.
‘Dan siyasar wanda yana cikin wadanda suka kafa APC, ya bar jam’iyyar ne bayan rasa tikitin yin takarar Gwamna a 2023 a wajen Sanata Uba Sani.
Rahoton ya ce Sani Sha’aban ya kaddamar da yakin takararsa a garin Tashan Yari da ke karamar hukumar Makarfi, ya yi alkawarin yaki da talauci.
Alkawarin 'dan takarar jam’iyyar ADP
Idan jam’iyyar ADP ta kafa gwamnati a jihar Kaduna a Mayun 2023, ‘dan takaran ya sha alwashin yakar talauci da rashin tsaron da ya addabi al’umma.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Hon. Sha’aban ya ce gwamnatinsa za ta ba manoma damar komawa gonakinsu.

Source: UGC
Tsohon ‘dan majalisar wakilan tarayyar na mazabar Zariya yake cewa ya shiga takarar Gwamnan ne domin ya taimakawa mutanen jihar Kaduna.
A cewar Sha’aban wanda ba yau ya fara takara ba, ya ce idan ya yi nasara a zabe mai zuwa, ba zai watsar da mutane kamar yadda ‘yan siyasa su ka saba ba.
Mafita ita ce ADP - Shugaban Jam'iyya
Kafin nan, an rahoto cewa shugaban jam’iyyar ADP na reshen Kaduna, Umar Isah ya ce mutanen jihar suna bukatar canji, kuma Sha’aban ne mafita a 2023.
Umar Isah ya yi kira da babbar murya da al’umma su yi waje da jam’iyyun APC da kuma PDP.

Kara karanta wannan
Bola Tinubu: Yadda Nayi Ta Lallabar Buhari, Har Aka Kara Wa’adin Canza Tsohon Kudi
“Mutanen jihar Kaduna su na burin canji, kuma Sha’aban ne zai kawo sauyi da ake bukata a jihar. Mafita ita ce a kawo ADP da Sha’aban kurum a zabe mai zuwa.”
A dalilin haka mu ka tuntubi Siraj Bamalli, daya daga cikin matasan da ke goyon bayan takarar Isa Ashiru Kudan a jam'iyyar PDP a jihar Kaduna.
Malam Siraj Bamalli ya shaida cewa tsayawa takarar Sha'aban ba wata barazana ba ce a halin yanzu domin jam'iyyar da ya fito ba ta shahara sosai ba.
A game da sauran jam'iyyun hamayya da suka fito neman mulki a 2023, matashin ya ce tasirin LP zai bayyana ne kurum a fgaruwan Kudancin Kaduna.
Ban tsoron kowa - Wazirin Adamawa
A ranar Talata aka samu labari cewa Atiku Abubakar ya nuna akwai yiwuwar jam’iyyarsa ta hada-kai da Rabiu Kwankwaso ko Peter Obi a zaben bana.
A tattaunawar da aka yi da shi, babban ‘dan takaran kujerar shugabancin Najeriyan ya ce mutane sun gaji da mulkin APC, kuma ya tabo batun zargin rashawa.
Asali: Legit.ng
