Gwamnan Babban Jihar Arewa Ya Faɗa Wa Ƴan Najeriya Wanda Ya Cancanta Su Zaɓa Shugaban Kasa A 2023

Gwamnan Babban Jihar Arewa Ya Faɗa Wa Ƴan Najeriya Wanda Ya Cancanta Su Zaɓa Shugaban Kasa A 2023

  • Aminu Bello Masari, gwamnan jihar Katsina ya ce babu wanda ya fi dacewa ya mulki a Najeriya a 2023 fiye da Bola Tinubu
  • Tsohon kakakin majalisar dokoki na tarayyar ya ce mutum ne mara nuna kabilanci ko tsatsauran ra'ayin addini kuma gogagge a bangarorin mulki, gina al'umma da sauransu
  • Masari ya kuma ce yana kyautata zaton jam'iyyar APC za ta ci zaben gwamna a Katsina saboda ayyukan da gwamnatinsa ta yi a shekaru 8 da suka gabata da cancantar dan takarar da jam'iyyar ta tsayar

Katsina - Gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari ya ce dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Asiwaju Bola Tinubu ne zabi mafi cancanta ga Najeriya a 2023.

Ya ce Tinubu ya dara sauran yan takarar shugaban kasar a bangarorin kafa tarihi, asali da ayyukan cigaba.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Surukin Shugaba Buhari Ya Sauya Sheka Daga APC, Ya Fadi Dalili

Bola Tinubu
Masari: Tinubu Ne Zabi Mafi Cancanta Ga Yan Najeriya A 2023. Hoto: @TheNationNews
Asali: Twitter

Masari ya furta hakan ne yayin wani hira ta musamman da ya yi da The Nation a ofishinsa da ke Katsina.

Ya bayyana Tinubu a matsayin wani abu mai daraja a kasar nan kuma zai cigaba da amfanar Najeriya idan aka zabe shi shugaban kasa.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

A cewar Masari:

"Tarihin Tinubu lokacin da ya ke ofis ya nuna ya dauki mutane daga kabilu daban-daban aiki, kuma tsohon sanata ne, mai bada tallafi, mai goyon bayan dimokradiyya kuma ana iya ganin wadanda suka amfana da shi.
"Ba a san shi da nuna kiyayya ba ko fifiko da kabilanci ko tsatsauran ra'ayin addini yayin da yana da wahala a gano abubuwan cigaban da abokan hamayyarsa suka yi baya ga yawon bude ido da biyewa yan kazangi."

Dalilin da yasa APC za ta ci zaben gwamna a Katsina - Masari

Kara karanta wannan

2023: Ya zama wajibi dukkan Musulmi ya zabi Tinubu, inji wata kungiyar Musulmai

A cewar rahoton na The Nation, Masari ya yi kira ga yan Najeriya su sani cewa zaben Tinubu a shekarar 2023 abu ne da ya zama dole saboda tsayayyiyar kasa da cigaba.

Game da yiwuwar nasarar APC a jihar Katsina, gwamnan ya ce cigaban da gwamnatinsa ta samu a shekaru takwas da suka gabata da cancantar dan takarar jam'iyyar zai tabbatar da samun nasarar jam'iyyar.

Zaben 2023: Sauran kiris in zama shugaban kasa, In Ji Tinubu

Asiwaju Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na APC ya ce saura matakai kadan ya zama shugaban kasa na gaba a Nigeria.

A cewar rahoton Vanguard, Tinubu ya furta hakan ne yayin tattaunawa da shugabannin darikar Tijaniyya a Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164

Online view pixel