Hotuna: Peter Obi Da Abokin Takararsa Baba-Ahmed Sun Ziyarci Sarkin Kano, Ya Bayyaan Abin Da Suka Tattauna

Hotuna: Peter Obi Da Abokin Takararsa Baba-Ahmed Sun Ziyarci Sarkin Kano, Ya Bayyaan Abin Da Suka Tattauna

  • Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na Labour Party, ya ziyarci Kano a yunkurinsa na samun goyon bayan yan arewa gabanin zaben 2023
  • Obi, tare da abokin takararsa Datti Baba-Ahmed, ya ziyarci Sarkin Kano Mai martaba Aminu Ado Bayero a ranar Asabar 24 ga watan Satumba
  • Tsohon gwamnan na jihar Anambra ya ce ya yi tattaunawa mai amfani da sarkin na Kano

Kano - Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party, LP, Peter Obi da abokin takararsa Datti Baba-Ahmed sun ziyarci Mai Girma Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero.

Obi, wanda ya wallafa rubutu da hotuna a shafinsa na Twitter a ranar Asabar ya ce 'an yi tattaunawa masu muhimmanci' tare da sarki.

Peter Obi ya ziyarci Sarkin Kano
Hotuna: Peter Obi Da Abokin Takararsa Baba-Ahmed Sun Ziyarci Sarkin Kano, Ya Bayyaan Abin Da Suka Tattauna. Hoto: @PeterObi
Asali: Twitter

Tsohon gwamnan na Jihar Anambra ya rubuta:

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kara karanta wannan

Atiku Ya Yi Magana Bayan Fallasar Wike, Ya Bayyana Yadda PDP Za Ta Ci Zabe A 2023

"Na ziyarci kasar Kano mai dumbin tarihi tare da abokin takara na, Yusuf Baba-Ahmed. Na samu damar ziyarar Mai Martaba Sarkin Kano Aminu Ado Bayero."

Obi kuma ya ziyarci Sarkin Gaya, Alhaji Aliyu Ibrahim kuma ya tattauna game da gobarar da ya faru a kasuwa da ambaliyar ruwa a Kano.

Tsohon gwamnan na jihar Anambra ya rubuta:

"Mun tattauna abubuwa masu muhimmanci da amfani, ciki har da gobarar da ta faru a kasuwar Kano da ambaliyar ruwa a arewa."

A bangare guda, yanayin shigar da Peter Obi ya yi ya dauki hankalin wani mai amfani da Twitter, Thεό Abu, @TheoAbuAgada, wanda ya ce bai ji dadin hakan ba.

Ya rubuta:

"Mai yasa wani zai ba wa Obi babban rigarsa domin ya dauki hoto ya yi kama da dan arewa?
"Wannan ba daidai bane kuma ya kamata a soki abin. A bar Obi ya zama Obi kuma a dena tilasta shi ya saka tufafin da bai saka daga gida ba. Ban ji dadi ba."

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Jerin Sunayen Jaruman Fina-Finan Najeriya 24 Da Suka Samu Shiga Kwamitin Kamfen Din Tinubu

2023: Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da PDP Ta Shigar Na Neman Haramtawa Tinubu Da Obi Yin Takara

A wani rahoton, babban kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta yi watsi da karar da jam'iyyar PDP ta shigar na neman a soke takarar Bola Tinubu na jam'iyyar APC da Peter Obi na Labour Party, The Cable ta rahoto.

A karar mai lamba FHC/ABJ/CS/1016/2022, PDP ta kallubalanci sauya yan yan takarar mataimakan shugaban kasa da APC da Labour Party suka yi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel