Atiku Ya Nada Sabon Mukami, Ya Kawo Wanda Zai Taya Shi Lashe Zaben Shugaban Kasa

Atiku Ya Nada Sabon Mukami, Ya Kawo Wanda Zai Taya Shi Lashe Zaben Shugaban Kasa

  • Paul Ibe ya sanar da cewa Alhaji Atiku Abubakar ya sake dauko wanda zai rika magana a madadin kwamitin neman zabe
  • ‘Dan takaran na shugaban kasa a jam’iyyar APC ya dauko Charles Aniagwu ya taimakawa Dino Melaye da Daniel Bwala
  • Charles Aniagwu kwararren ‘dan jarida ne wanda ya san kan aiki, yayi shekara da shekaru yana wannan harka a jihar Delta

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Abuja - ‘Dan takarar kujerar shugabancin Najeriya a inuwar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya bada sanarwar nadin mukami a kwamitin kamfe.

Business Day ta kawo rahoto cewa Charles Aniagwu ya zama Kakakin kwamitin yakin neman takarar Alhaji Atiku Abubakar da jam’iyyar PDP.

A ranar Talata, 6 ga watan Satumba 2022 aka samu labari Mista Aniagwu ya shiga cikin wadanda za su rika magana da yawun kwamitin zaben.

Kara karanta wannan

APC ta Dakatar da Tsohon Mataimakin Shugaban Majalisa Saboda Ya Hada-kai da PDP

Atiku Abubakar ya bada wannan sanarwa ne a wani jawabi da ya fito daga bakin Paul Ibe.

Ibe yace Aniagwu zai fara aiki ba tare da bata lokaci ba, zai bada gudumuwa wajen sanar da al’umma game da yakin neman zaben Atiku a 2023.

Atiku
Atiku Abubakar, Okowa da Ayu Hoto: @Atikuorg
Asali: Twitter

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“Aniagwu ya san kan aiki”

“Charles Aniagwu kwararren ‘dan jarida ne wanda ya shafe fiye da shekaru 20 yana aiki a kafofin yada labarai.
“Za iyi aiki tare da sauran wadanda aka bada sanarwar su ne masu magana da yawun bakin kwamitin kamfe”

- Paul Ibe

Da wannan sanarwa, ‘dan jaridar zai yi aiki tare da Sanata Dino Melaye da Daniel Bwala, wadanda zuwa yanzu sune ke magana da yawun kwamitin.

Asali Daniel Bwala Lauya ne, shi kuwa Dino Melaya yayi digir ne a ilmin kasa.

Mutumin Gwamna Ifeanyi Okowa

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Shugaban 'yan sanda ya magantu kan yiwuwar yin zabe a shekara mai zuwa

Yanzu haka Charles Aniagwu shi ne Kwamishinan harkokin yada labarai a jihar Delta. Idan ba a manta ba, daga Delta Atiku ya dauko abokin takara.

Gwamna Ifeanyi Okowa ne ya nada Aniagwu a matsayin kwamishinan labarai, kafin nan ya rike masa kujerar babban sakataren Gwamna a jihar Delta.

Likitoci sun bi LP a 2023

Dazu kun ji labari shugaban kungiyar Docs and Medics for Peter Obi ya yi bayanin dabarar da za a bi domin kai Jam’iyyar Labour Party ga nasara a 2023.

Uche Uzoukwu yace sun fara ratsa lunguna da sako, ana karkato da ra’ayin marasa lafiya domin su zabi Peter Obi, kuma a kawo masa kuri’a miliyan 25.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng