2023: Tsohon Sanata da tsohon Minista sun shiga NNPP a Jihohin Taraba da Bauchi

2023: Tsohon Sanata da tsohon Minista sun shiga NNPP a Jihohin Taraba da Bauchi

  • Sanata Isa Hamma Misau ya sanar da sauya-shekarsa daga jam’iyya mai mulki zuwa NNPP
  • A Taraba, jam’iyyar NNPP ta samu ‘Yan Majalisa biyu da tsohon Minista, Sanata Joel Ikenya
  • Yayin da ake shirin zaben 2023, NNPP ta su Rabiu Kwankwaso ta na kara shiga Arewa ta gabas

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Bauchi - Siyasar jihar Bauchi ta na cigaba da canza salo yayin da Sanata Isa Hamma Misau ya sake canza-sheka, wannan karo zuwa jam’iyyar NNPP.

Kamar yadda Legit.ng Hausa ta gani a Facebook, Isa Hamma Misau ya hadu da Rabiu Musa Kwankwaso a yammacin Alhamis, 14 ga watan Yuli 2022.

A haduwar Sanata Isa Misau da ‘dan takaran shugaban kasar na 2023, ya tabbatarwa Duniya shigarsa cikin jam’iyyar ta NNPP mai alamar kayan marmari.

Misau ya wakilci mazabar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa a APC, daga baya ya shiga PDP.

Kara karanta wannan

2023: Na-hannun daman babban Ministan Buhari yana yi wa PDP aiki a maimakon APC

Isa Hamma Misau da Yakubu Dogara su na cikin wadanda suka bar PDP kwanakin baya, suka sake komawa jam’iyyar APC mai mulki da suka bari a da.

Yanzu NNPP ta na da Sanatoci masu-ci biyu daga Bauchi, Dauda Halliru Jika da Tijjani Gumau duk sun bada sanarwar ficewarsu daga jam'iyyar APC.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Tsohon Sanatan Bauchi
Isa Hamma Misau da Rabiu Kwankwaso Hoto: Saifullahi Hassan
Source: Facebook

NNPP ta yi kamu a Taraba

A jihar Taraba kuma, akwai rade-radin cewa Hon. Rimamde Shawulu ya fita daga jam’iyyar PDP mai mulkin jihar, shi ma ya koma jam’iyyar adawa ta NNPP.

Yanzu haka Shawulu ne ‘dan majalisan mazabun Dunga/Takun/Ussa/Yangtu a majalisar tarayya. Shi ma ‘dan majalisar jiha, Hon. Nasir Tafida ya bi shi.

Haka zalika ta tabbata Joel Danlami Ikenya ya sauya-sheka zuwa NNPP. Ikenya babban ‘dan siyasa ne wanda ya nemi kujerar Gwamna sau uku a jihar.

Tsakanin 1992 zuwa 1993, Ikenya yana majalisar dokokin Taraba. A 1999 kuma aka zabe shi a matsayin ‘dan majalisar wakilan tarayya, ya zarce har 2007.

Kara karanta wannan

PDP ta kai INEC Kotu, ta bukaci a haramtawa Tinubu, Peter Obi neman Shugaban kasa

Har ila yau, Joel Danlami Ikenya ya rike kujerar Sanatan Kudancin jihar Taraba zuwa 2011. Daga nan ya fara neman zama Gwamna a PDP amma bai dace ba.

Da Darius Ishaku ya zama ‘dan takaran Gwamna a PDP, Ikenya ne aka zaba ya maye gurbinsa a gwamnatin tarayya, ya zama Ministan kwadago zuwa 2015.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng