Kai Tsaye: Yadda Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Yau Asabar

Kai Tsaye: Yadda Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Yau Asabar

A yau Asabar, 16 ga watan Yuli, 2022, hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa wato INEC zata gudanar da zaɓen gwamna jihar Osun.

Wa'adin zangon farko na gwamna mai ci, Gboyega Oyetola, na jam'iyyar APC ya zo karshe kuma al'ummar jihar zasu fito su zabi wanda zai cigaba da jagorantar su na tsawon shekara hudu.

Yan takarar da ake ganin suna sahun gaba a zaɓen sune;

1. Gwamna mai ci, Gboyega Oyetola, na jam'iyyar APC wanda ke neman tazarce

2. Ademola Adeleke na jam'iyyar PDP

3. Yusuf Lasun na jam'iyyar Labour Party LP

4. Rasaq Saliu na jam'iyya mai kayan marmari NNPP

Legit.ng Hausa ta shirya zata kawo muku duk abinda ke gudana kama daga shirye-shirye, yadda zaɓen zai gudana har zuwa lokaci da bayan sanar da sakamako.

Yarjejeniyar zaman lafiya

A ranar Laraba jam'iyyu 13, da suka haɗa da manyan jam'iyyyu APC da PDP, suka rattaɓa hannu a kan yarjejeniyar zaman lafiya tare da alƙawarin zasu nisanci ta da yamutsi yayin da kuma bayan zaɓe.

Shugaban hukumar zaɓe, Farfesa Mahmud Yakubu, ya yi kira ga yan takara, jam'iyyu da sauran masu ruwa da tsaki a wurin taron cewa sa hannun su bai isa ba, abinda ya fi muhimmanci shi ne bin abubuwan da yarjejeniyar ta ƙunsa.

Dan takarar PDP, Ademola Adeleke ya lashe zabe

Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ta ayyana Dan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP),Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Osun.

Baturen zabe a jihar, Toyin Ogundipe, ne ya sanar da sakamakon zaben a safiyar ranar Lahadi, 17 ga watan Yuli, jaridar The Cable ta rahoto.

Adeleke ya samu kuri’u 403, 371 wajen lallasa babban abokin hamayyarsa Gboyega Oyetola na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), wanda ya samu kuri’u 375,027.

Sakamakon karamar hukumar Oriade

A 60

AAC 66

ADP 382

APC 14189

LP 24

PDP 15947

Sakamakon karamar hukumar Ife ta kudu

APC= 12,481

LP= 28

PDP= 9,116

Sakamakon karamar hukumar Ife ta gabas

APC= 19,353

LP= 65

PDP= 18,071

Sakamakon ƙaramar hukumar Ife ta kudu

APC: 12,481

PDP: 9,116

Sakamakon ƙaramar hukumar Ede ta arewa

APC: 9,603

PDP: 23,931

Sakamakon karamar hukumar Ife ta arewa

A: 74

AAC: 70

ADP: 341

APC: 9,964

APM: 50

APP: 24

BP: 14

LP: 4

NNPP: 11

NRM: 18

PDP: 10,359

PRP: 35

SDP: 9

YPP: 37

ZLP: 10

Sakamakon ƙaramar hukumar Ede ta kudu

A: 38

AAC: 43

ADP: 226

APC: 5,704

APN: 25

APP: 20

BP: 18

LP: 16

NNPP: 15

NRM: 57

PDP: 19,438

PRP: 33

SDP: 11

YPP: 37

ZLP: 10

Sanata mai rawa ya yi nasara a garuruwa 5

Alkaluma sun tabbatar da cewa ‘Dan takaran PDP, Ademola Adeleke ya samu nasara a kananan hukumomi biyar a zaben Gwamnan jihar Osun.

Jaridar Daily Trust ta ce PDP ta samu galaba a kan APC a kananan hukumomi Atakumosa ta yamma, Ifelodun, Orolu, Odo-Otin da Osogbo.

Adeleke ya na da kuri’u 79,453, Gwamna Gboyega Oyetola APC ya samu kuri’u 69,031. Tazarar kuri’a 10, 400 aka samu daga kananan hukumomin.

Sakamakon ƙaramar hukumar Ayedade

APC: 14,527

PDP: 13,380

Sakamakon ƙaramar hukumar Ife Central

A: 202

AAC: 145

ADP: 374

APC: 17880

APM: 59

APP: 21

BP: 10

LP: 134

NNPP: 14

NRM: 29

PDP: 13532

PRP: 42

SDP: 50

YPP: 44

ZLP: 08

Tsagerun sun jawo an daina tattara kuri’u

Tsageru sun kawo matsala a yayin da hukumar INEC ta ke kokarin tattara sakamakon kuri’un zaben Gwamnan Osun.

Hakan ya faru ne a karamar hukumar Ife ta Gabas kamar yadda jaridar Premium Times ta fitar da rahoto da yamman nan.

A dalilin haka, ma'aikata sun dakatar da tattara sakamakon kuri’un da aka samu daga rumfunan zaben da ake da su a yankin.

Sakamakon karamar hukumar Boripe

A - 91

AAC - 82

ADP - 355

APC - 21205

APM - 56

APP - 25

BP - 05

LP - 04

NNPP - 07

NRM - 13

PDP - 7595

PRP - 24

SDP - 09

YPP - 32

ZLP - 07

Sakamakon karamar hukumar Olorunda

A: 208

AAC: 95

ADP: 460

APC: 18709

APM: 40

APP: 23

BP: 19

LP: 63

NNPP: 17

NRM: 30

PDP: 21350

PRP: 56

SDP: 46

YPP: 51

ZLP: 20

Sakamakon karamar hukumar Atakumosa ta gabas

APC: 6,601

PDP: 7,750

Sakamakon Karamar Hukumar Edjigbo

APC: 8,919

PDP: 11,878

A: 41

AAC: 44

ADP: 282

APM: 39

BP: 9

LP: 23

NNPP: 11

NRM: 30

PRP: 36

SDP: 15

Sakamakon karamar hukumar Odo-Otin

APC: 13,482

PDP: 14,003

Sakamakon karamar hukumar Orolu

A : 69

AAC: 55

ADP: 271

APC: 9928

APM:21

APP:14

BP: 15

LP: 32

NNPP: 04

NRM: 14

PDP: 10282

PRP: 18

SDP: 09

YPP: 23

ZLP: 10

Sakamakon karamar hukumar Iwo

APC 17,421

PDP 16, 914

Sakamakon karamar hukumar Ifelodun

AAC - 93

ADP - 487

APC - 16,068

APM - 45

APP - 13

BP - 07

LP - 18

NNPP - 13

NRM - 17

PDP - 17,107

PRP - 31

SDP - 12

YPP - 47

ZLP – 13

Sakamakon karamar hukumar Osogbo

AAC: 130

ADP: 617

APC: 22,952

APM: 55

APP: 47

BP: 18

LP: 79

NNPP: 22

NRM: 48

PDP: 30,401

PRP: 70

SDP: 62

YPP: 79

ZLP: 22

Sakamakon karamar hukumar ILA

APC- 11163

PDP- 13036

Sakamakon karamar hukumar Ilesa ta yamma

AAC: 77

ADP: 407

APC: 10,777

APM: 48

APP: 22

BP: 09

LP: 40

NNPP: 13

NRM: 16

PDP: 13,769

PRP: 45

SDP: 21

YPP: 33

ZLP: 20

Gudunmar (RA): Oke ObaII, karamar hukumar Iwo

AAC: 14

ADP: 78

APC: 1833

APM: 04

APP: 08

BP: 00

LP: 03

NNPP: 03

NRM: 05

PDP: 1489

PRP: 08

SDP: 03

YPP: 11

ZLP: 03

An fara tserewa APC

A sakamakon zaben da aka fitar zuwa yanzu, Ademola Adeleke ne a gaba, ya ba Gwamna Gboyega Oyetola na APC rata.

Adeleke ya na da kuri’u 67,892 shi kuma Oyetola ya samu 56,915. Rahoton Daily Trust ya ce akwai ratar kusan kuri’a 11, 000.

Hukumar INEC ta na cigaba da tattara kuri’u

PDP ta lashe karamar hukuma 1

Sanata Ademola Adeleke na PDP ne aka tabbatar a matsayin wanda ya lashe zaben Gwamnan Osun a karamar hukumar Atakumos ta Yamma.

INEC ta ce ‘Dan takaran yana da kuri’a 7750, Gwamna Gboyega Oyetola da jam’iyyar APC ne suka zo na biyu da ratar kuri’a 1, 149 da kuri’u 6601.

Gunduma ta 3, Olugun Agbaakin, Karamar Hukumar Ede ta Arewa

APC: 1676

PDP: 1694

Gunduma ta 3, Isale Oba 3, Karamar Hukumar Iwo

APC: 1237

PDP: 1656

Gunduma ta 6, Ikire F, Karamar Hukumar Irewole

APC: 1990

PDP: 1829

Gunduma ta 15, Oke Oba 2, ƙaramar hukumar Iwo

APC: 1833

PDP: 1489

Gunduma ta 10, ƙaramar hukumar Ede ta kudu

APC: 361

PDP: 1130

Gunduma ta 007 Molete 3, ƙaramar hukumar Iwo

APC: 1585

PDP: 1477

Gunduma ta 001 Ikire A, karamar hukumar Irewole

APC: 1509

PDP: 1120

Gunduma ta 001, ƙaramar hukumar Ede ta kudu

Adadin masu kaɗa kuri'a: 6273

Adaɗin waɗan da aka tantance: 3242

A: 9

AAC: 8

ADP: 20

APC: 679

APN: 3

APP: 1

BP: 2

LP: 2

NNPP: 0

NRM: 5

PDP: 2443

PRP: 2

SDP: 6

YPP: 2

ZLP: 0

Jumullar halastattun kuri'u: 3182

Kuri'un da suka ɓaci: 49

Gunduma ta 04 Atelewo, ƙaramar hukumar Olorunda

Masu kaɗa kuri'a: 7371

Waɗan da aka tantance: 2935

A: 19

AAC: 3

ADP: 24

APC: 1370

APM: 2

APP: 2

BP: 1

LP: 4

NNPP: 03

NRM: 3

PDP: 1443

PRP: 8

SDP: 02

YPP: 2

ZLP: 1

Halastattun kuri'u: 2875

Kuri'un da suka lalace: 60

Jumullan kuri'un da aka kaɗa: 2935

Gunduma ta 10, Eyindi/Ipirin, ƙaramar hukumar Ila

A- 04

AAC- 03

ADP- 19

APC- 675

APM- 02

APP- 00

BP- 00

LP- 00

NNPP- 00

NRM- 02

PDP- 825

PRP- 01

SDP- 01

YPP- 01

ZLP- 01

Sakamakon gunduma ta 11 a ƙaramar hukumar Atakumosa ta yamma

Adadin masu katin zaɓe - 2714

Adadin mutanen da aka tantance - 936

A- 2

AAC-4

ADP-10

APC-593

APM-1

APP-0

BP-1

LP-1

NNPP-0

NRM-2

PDP-288

PRP-3

SDP-0

YPP-2

ZLP-0

Jimullan kuri'un da aka kaɗa - 907

Ƙuri'un da ba'a jefa dai-dai ba - 17

Sakamakon gunduma ta 03 Ikeija II, Ife ta kudu LGA

Masu rijistar zaɓe – 3443

Masu kaɗa kuri'a da aka tantance – 1699

A: 01

AAC: 0

ADP: 27

APC: 821

APM: 03

APP: 0

BP: 0

LP: 01

NNPP: 01

NRM: 01

PDP: 801

PRP: 01

SDP: 0

YPP: 01

APC ta rasa gidan Gwamnati

Sakamakon zabe ya tabbatar da cewa akwatin da ke gaban gidan gwamnati ya fada hannun ‘Dan takarar jam’iyyar PDP, Sanata Ademola Adeleke.

Adeleke ya doke Gwamna Oyetola a rumfar gidan Gwamnati, PDP ta samu kuri’u 117, APC ta na da 106 yayin da ake cigaba da tattara sakamako.

Sakamakon rumfa ta 08, gundumar Oba Isale 2, Iwo LGA

APC: 73

PDP: 55

Gudunma ta 07, akwatin zabe ta 001, karamar hukumar Olorunda

ADP 03

APC 150

PDP 140

Akwatin Zabe na 017, Gundumar Alagba, Karamar Hukumar Osogbo

ADP - 02

APC - 89

A - 0

AAC - 0

PDP - 92

LP - 0

PRP - 0

Gwamna Oyetola ya lashe rumfar zaɓensa

Gwamnan jihar Osun, Gboyega Oyetola ya lashe zaɓe a rumfar zaben da ya ke kaɗa kuri'a da gagarumin rinjaye inda ya samu kuri'u 545.

Sakamakon zaɓe a rumfa ta 02, gunduma ta, 01, ƙaramar hukumar Boripe

APC - 545

PDP - 69

Sakamakon zaben rumfa ta 5, gunduma ta 4 a karamar hukumar Ilesa ta Gabas

Sakamakon zaben gwamnan jihar Osun daga rumfa ta 5 a gunduma ta 4; Itisan/Ogudu, karamar hukumar Ilesa ta Gabas.

A- 01

AAC-01

ADP- 04

APM-1

APC - 96

PDP - 59

PRP-01

Sakamakon zabe su na ta shigowa

  • Sakamakon zabe daga karamar hukumar Ife ta Tsakiya

Akwati na 3 (Post Office)

ADP 02

APC 116

PDP 103

  • Sakamakon zabe daga karamar hukumar Ife ta Kudu

Akodi Famoroti Ifetedo

Ikija 1

APP: 0

AAC: 0

ADP: 01

APC: 65

APM: 0

APP: 0

BP: 0

LP: 0

NNPP: 0

NRM: 01

PDP: 70

PRP: 0

SDP: 0

YPP: 0

ZLP: 0

  • Sakamakon zabe daga karamar hukumar Ife ta Arewa

Garin Yakoyo, Ife

AAC- 01

ADP- 01

APC- 103

PDP - 113

LP- 02

NRM- 01

  • Sakamakon zabe daga karamar hukumar Ilesa ta Yamma

APP - 01

AAC- 01

ADP - 03

APC - 89

PDP - 154

YPP - 01

Rumfa ta 2, cibiyar kasuwa ta Moro

Sakamakon zaben gwmanan jihar Osun daga rumfa ta biyu a cibiyar kasuwa ta Moro da ke karamar hukumar Ife ta Arewa.

A- 2

AAC- 0

ADP- 5

APC- 101

PDP - 129

Sakamakon zabe daga karamar hukumar Ede ta Arewa

Sakamakon zabe daga rumfar Oba da ke karamar hukumar Ede ta Arewa; PU 004, Ward 08, Isibo/Buari-Isolo:

APC: 44

PDP: 131

Gunduma ta 4, Akwatin Zabe ta 6, Karamar Hukumar Iwo

Sakamakon zabe daga Gunduma ta 4, Akwatin Zabe ta 6, Karamar Hukumar Iwo

ADP 07

PDP 178

APC 176

Gunduma ta 4, Akwatin Zabe ta 4, Karamar Hukumar Iwo

ADP 07

PDP 98

APC 46

LP 11

Sakamakon zabe

PU 004, Fajuyi Hall OAU, Gunduma ta 05, Iremo/Ajebamidele, Karamar Hukumar Ife Central

PDP: 28

APC: 29

Accord: 9

LP: 2

Sakamakom zaɓe daga runfunan zaɓe sun fara bayyana

PU 4: ƙauyen Elepo, gundumar Bode-Osi ta 008, Olaoluwa LGA

APC: 38

PDP: 96

AAC: 2

PRP: 01

YPP: 01

Masu rijistar zaɓe: 329

Kuri'un da aka kaɗa: 141

Kuri'un da suka lalace : 03

Sakamako: Runfar zaɓe ta 29, gunduma ta 008, Olorunda LGA

PDP - 91

APC - 39

ACCORD - 1

YPP - 1

ADP - 3

APM - 1

SDP – 1

Kuri'un da suka lalace: 02

Sakamako: Rumfar zaɓe ta 5, gunduma ta 5, salvation Army, Oke fia, Osogbo

APC- 121

PDP -196

ADP-2

ZLP-1

SDP-1

Accord- 4

AAC - 1

PU 004, Fajuyi Hall OAU, gunduma ta 05, Iremo/Ajebamidele, Ife Central LGA

PDP: 28

APC: 29

Accord: 9

LP: 2

Ma'aikatan INEC na jiran lokacin rufe zaɓe

Wani Hoto da The Cable ta wallafa ya nuna yadda wasu ma'aikatan wucin gadi da ke aikin zaɓe a jihar Osun suka fara gyangyaɗi yayin da suke jiran lokacin karkashe zaɓe a hukumance.

An ɗauki Hoton ne a Rumfar Zaɓe ta 008, gunduma ta 007 a Ipetumodu 2, ƙaramar hukumar Ife ta arewa a jihar Osun.

Wata Runfar zaɓe a Osun.
Kai Tsaye: Yadda Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Yau Asabar Hoto: @thecable
Asali: Twitter

Jami'an tsaro sun kama 'yan daba da bindigu

Yayin da zaɓe ya yi nisa a jihar Osun, jami'an tsaro sun yi nasarar damƙe wasu yan daba ɗauke da bindigu da ake zargin suna shirin ta da zaune tsaye.

Kudi kawai suke karba, ban ga kowani kuri’a ba, jami’in jam’iyya ya koka

Jami’in wata jam’iyyar siyasa a jihar Osun ya koka kan cewa mutane na karbar kudi ne kawai amma basu kada kowani kuri’a ba.

A cikin wani bidiyo da jaridar The Cable ta wallafa a shafin Twitter an jiyo jami’in na magana a harshen Yarbanci inda yake tambayar mutane jam’iyyunsu.

Gwamna Oyetola ya jinjinawa INEC kan yadda ake zabe cikin lumana

Gwamnan jihar Osun kuma dan takarar jam’iyyar APC, Adegboyega Oyetola, ya jinjinawa hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) kan yadda ake gudanar da zaben cikin lumana.

Ya bayyana hakan ne bayan ya kada kuri’arsa a zaben.

Mai nakasa zai kada kuri'a

Wani mai nakasa yayin da ake tantance shi domin ya kada kuri’arsa a zaben Gwamnan jihar Osun.

Hukumar INEC ta na amfani da na’urar BVAS ne wajen tantance fuskar masu kada kuri’a a zaben Gwamna.

An dauki hoton ne a Ikire, a karamar hukumar Irewole.

Hoto: @INECNigeria

Dan takarar APC, Oyetola da matarsa sun kada kuri'arsu

Gwamnan jihar Osun kuma dan takarar gwamna na jam'iyyar APC, Gboyega Oyetola da matarsa sun kada kuri'arsu.

Gwamnan dai yana takara ne domin neman wa'adi na biyu na gwamnan jihar.

Tsohuwa mai shekaru 80 ta fito ta kada kuri’a

Wata tsohuwa mai shekaru 80, Sidikatu Yusuf ta bayyana cewa ta damu da ci gaban Osun, inda ta ce wannan ne babban dalilinta na fitowa domin kada kuri’a a zaben.

Mawaki Davido: Mutane sun ki yarda su siyar da kuri’unsu

Mawakin Davido Adeleke wanda ya kasance 'da a wajen dan takarar PDP a zaben gwamnan na Osun, ya yi ikirarin cewa masu zabe sun ki karbar kudi don sayar da kuri’unsu.

Rikici ya barke a wata runfar zaɓe

Bidiyon yadda jami'an tsaro ke kokarin kwantar da hankulan fusatattun masu kaɗa kuri'a a runfar zaɓe ta 002, gunduma ta 001, ƙaramar hukumar Atakumosa.

Dattijo Mai Shekaru Fiye Da 90 Ya Jefa Kuri'arsa a Zaben Osun

Mustapha Olatunji, wani dattijo wanda ya haura shekaru 90 ya jefa kuri'arsa a karamar hukuma Boripe, Gunduma ta 1, Akwatin zabe na 002 a zaben gwamnan Osun.

Olatunji ya bayyana cewa tun zamanin tsohon firimiyan yankin yamma, Obafemi Awolowo ya ke zabe.

Tsohuwa ta kada kuri'a

Dazu aka ji cewa wata tsohuwa mai shekara 92 a Duniya, ta kada kuri'arta a akwatin zaben da ke makarantar firamaren Baptist Primary School a Isore/Ikonifin.

Kamar yadda INEC ta bayyana, wannan Baiwar Allah ta yi zaben ne a akwati na biyu da ke rumfa ta shida a Isore/Ikonifin da ke karamar hukumar Ola-Oluwa.

Dan takarar PDP, Ademola Adeleke, ya kaɗa kuri'arsa

Ɗan takarar gwamna ƙarƙashin jam'iyyar PDP, Sanata Ademola Adeleke, ya jefa ƙuri'arsa a zaɓen gwamnan Osun da ke gudana yanzu haka.

Sanata Adeleke ya kaɗa kuri'arsa ne a runfar zaɓe ta 009, gunduma ta 002, Abongunde/Sagba, a ƙaramar hukumar Ede ta arewa.

Sanata Ademola Adeleke.
Kai Tsaye: Yadda Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Yau Asabar Hoto: Punch
Asali: Twitter

An fara kada kuri'a a rumfar dan takarar gwamnan APC a Osun

Yanzu haka an fara kada kuri'a a zaben gwamnan Osun, a rumfa ta 02, unguwa ta 1, Popo, Iragbiji a karamar hukumar Boripe LGA.

Rumfar dai ita ce ta inda dan takarar gwamna a jam'iyyar APC a zaben jihar yake.

Zaben Osun 2022
Kai Tsaye: Yadda Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Yau Asabar | Hoto: TheCable
Asali: Twitter

Jami'ai INEC sun fara tantance masu kaɗa kuri'a

Ana gab da fara jefa kuri'a yayin da mutum na farko ya gabatar da kansa ga jami'an wucin gadi domin tantance shi a PU 1, Ward 3, makarantar Methodist, karamar hukumar Atakumosa ta yamma, jihar Osun.

An fara tantance masu kaɗa kuri'a.
Kai Tsaye: Yadda Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Yau Asabar Hoto: INECNigeria
Asali: Twitter

Jami'an wucin-gadi na INEC suna dub sunayensu a ofishin INEC

Jami'an wucin-gadi na hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, wadanda suka hada da masu hidimar kasa, sun duba sunayensu a ofishin hukumar zaben dake kan titin Ilobu a karamar hukumar Osogbo domin sanin inda ake tura su aikin zaben.

INEC Staff
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana
Asali: Original

INEC Staff
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana
Asali: Original

INEC Staff
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana
Asali: Original

Mutane sun fara fitowa kaɗa kuri'a

Tuni masu ƙaɗa kuri'a suka fara tururuwa runfunan zaɓe domin kaɗa kuri'un su. A runfar zaɓe ta 1, gundumar Alajue 5, Aisu yankin Ede, mutanen da suka fito na zaune yayin da jami'an INEC ke shirye-shirye domin fara jefa kuri'a.

Wasu Hotuna da jaridar Vangaurd ta tattaro sun nuna yadda masu kaɗa kuri'u ke zaune yayin da matasa yan bautar ƙasa ke shiryawa don fara aikin su na wucin gadi.

Masu kaɗa kuri'a a zazzaune.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: @vanguardngr
Asali: Twitter

Masu kaɗa kuri'a.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: vanguardngr
Asali: Twitter

Ma'aikatan INEC na shiryawa.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: @vanguardngr
Asali: Twitter

Jami'an tsaro sun mamaye muhimman wurare a Osun

Jam'an tsaron Najeriya da suka haɗa da Sojoji, Yan sanda, Dakarun Cibil Defence sun mamaye manyan muhimman wurare a ilahirin babban birnin Osun da kuma garuruwa masu iyaka.

Hukumar yan sanda ta girke dakaru 21,000 don tabbatar da komai ya tafi cinin tsaro yayin zaɓen kuma ta gargaɗi duk wani me shirin tada zaune tsaye ya nesanci runfunan zaɓe.

Haka nan kuma hukumar tsaro ta Cibil Defence wato NSCDC ta ce ta jibge dakaru 11,000 kuma ta tabbatar wa mazauna jihgar da cewa zasu samu kariya.

Jami'an tsaro sun mamaye Osun.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: @thecable
Asali: Twitter

Yan sanda sun shirya.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: @thecable
Asali: Twitter

Dakarun yan sanda a Osun.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: thecable
Asali: Twitter

Dakarun yan sanda yayin sinitiri a Osun.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: thecable
Asali: Twitter

Zamu karɓi kuɗi, mu zaɓi wanda muke so - Mazauna Osun

Yayin da komai ya kankama na zaɓen gwamnan jihar Osun yau Asabar, wasu daga cikin mazauna jihar sun shaida wa manema labarai cewa zasu tabbata sun zaɓi ɗan takarar da suke so.

Legit.ng Hausa ta fahimci cewa aƙalla mutum miliyan 1,955,657 suka yi rijistar zaɓe kuma ake tsammanin zasu kaɗa kuri'un su a runfunan zaɓe 3,763 dake faɗin jihar.

Haka nan ana tsammanin mutane zasu fito zaɓe kwansu da kwarkwata fiye da yadda suka fito a zaɓen 2018 da ya gabata.

Wani mazaunin Osun, Kunle Ogundele, ya ce: "Mutane zasu yi tururuwa su fito duk da akwai ƙalubalen sayen kuri'a. Zamu karɓi kudin su, kuma mu dangwala wa wanda zuciyarmu take so."

Demola Ahmed, wani mazaunin jihar ya ce mutane zasu fito duk da matakan tsaron da aka jibge suke aiki sintiri don tabbatar da tsaro a cikin gari.

Jam'iyyar AD ta ayyana goyon bayan gwamna Oyetola

Jam'iyyar Alliance for Democracy (AD) ranar Jummu'a ta ayyana cikakken goyon bayanta ga tazarcen gwamna Gboyega Oyetola, ɗan takarar jam'iyyar APC a zaɓen gwamnan Osun.

Hukumar dillancin labarai ta ƙasa (NAN) ta tattaro cewa jam'iyyar AD na ɗaya daga cikin jam'iyyun siyasa a Najeriya da hukumar zaɓe ta ƙasa INEC ta soke rijistar su.

A wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun shugaba da Sakataren tsare-tsare, jam'iyyar AD ta umarci mambobinta, masoya da magoya baya su yi tururuwa don kaɗa wa Oyetola kuri'un su.

Gangamin taron masoyan Oyetola.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: Kebbi State Government
Asali: Facebook

An jibge jami'an yan sanda a jihar Osun

Bidiyon jami'an hukumar yan sanda waɗan da aka tura yin aiki yayin zaɓen gwamnan jihar Osun wanda zai gudana gobe Asabar, 16 ga watan Yuli, 2022.

INEC ta kammala rarraba kayan zaɓe

Hukumar zaɓe INEC ta bayyana cewa ta gama shiri tsaf na gudanar da zaɓen gwamnan Osun, ɗaya daga cikin jihohin yankin kudu maso yammacin Najeriya.

Yayin da ya rage awanni a fita runfunan zaɓe, INEC ta ce tuni ta kammala rarraba kayayyakim zaɓe zuwa ƙananan hukumomin jihar guda 30 a gaban jami'an tsaro.

Jami'ar INEC, Hajiya Zainab Aminu, ta shaida wa BBC Hausa cewa sun gama raba kayayyaki da suka haɗa da takardun kaɗa kuri'a da na rubuta sakamako cikin nasara.

A cewarta, dukkan kayayyakin da suka tura zuwa kananan hukumomi 30 sun isa lafiya ba tare da samun wata matsala ba.

Raba kayan zaɓe a Osun.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: INEC Nigeria
Asali: Twitter

Raba kayan aiki.
Kai Tsaye: Yadda Shirye-Shiryen Zaɓen Gwamnan Jihar Osun Ke Gudana Hoto: INEC Nigeria
Asali: Twitter

Tags:
Online view pixel