Rochas Okorocha da wasu Sanatoci 3 da za su yi takarar Shugaban kasa a zaben 2023

Rochas Okorocha da wasu Sanatoci 3 da za su yi takarar Shugaban kasa a zaben 2023

  • Ana kyautata zaton wanda zai rikewa APC tuta a zaben shugaban kasan 2023 zai fito ne daga kudu
  • Hakan ta sa aka samu wasu ‘Yan majalisa daga kudancin Najeriya da suke shirin tsayawa takara
  • Wadannan Sanatoci sun yi fice a siyasa, kuma an yi shekaru ana gwabzawa da dukkaninsu a siyasa

Abuja - A rahoton na mu na yau, mun tattaro sunayan ‘yan majalisar dattawan da aka san su na da shirin tsayawa takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC.

Jerin yana dauke da Sanatoci da suke a kan mulki a yau. Baya ga wadannan akwai wasu tsofaffin Sanatocin da za su shiga neman takarar shugaban kasar.

A cikin wadanda suka taba rike kujerar Sanata da suke harin shugabancin Najeriya a 2023 akwai Anyim Pius Anyim, Bukola Saraki da Asiwaju Bola Tinubu.

Kara karanta wannan

Sabuwar dokar APC ta baiwa Amaechi, Ngige awanni 72 su yi murabus ko su hakura da takararsu

Haka zalika akwai irinsu Rabiu Musa Kwankwaso wanda zai yi takara a karkashin jam’iyyar NNPP.

Jerin Sanatocin

1. Rochas Okorocha

Sanatan Imo ta yamma a majalisar dattawa, Rochas Okorocha yana sha’awar fitowa takarar shugaban kasa a APC a zaben da za a shirya kwanan nan.

Ba wannan ne karon farko da tsohon gwamnan na jihar Imo ya nemi tikitin yin takarar shugaban kasa ba. Okorocha yana sa ran ya kai labari a zaben 2023.

Majalisa
Zaman majalisar dattawa Hoto: @NgrSenate
Asali: Facebook

2. Orji Uzor Kalu

A jerin na mu akwai Sanata Orji Uzor Kalu wanda yanzu haka shi ne mai wakiltar mutanen Arewacin jihar Abia a majalisar dattawa a karkashin APC.

Shi ma Orji Uzor Kalu tsohon gwamna ne a Abia, kuma ya taba yin takarar shugaban kasa a jam’iyyar PPA, a lokacin Ummaru ‘Yar’adua ya lashe zabe.

Kara karanta wannan

Akwai yiwuwar APC ta hana Amaechi, Ngige, Malami da wasu Ministoci yin takara

3. Ibinkunle Amosun

A ranar Larabar nan aka ji labari Ibinkunle Amosun zai nemi takarar Shugaban kasa. Sanatan na Ogun ta tsakiya shi ne na karshe da ya ayyana burinsa a APC.

Kamar sauran abokan aikinsa, Amosun ya yi shekaru takwas yana gwamna a Ogun. Sanatan ya ce idan ya karbi shugabancin Najeriya, zai kai kasar ga ci.

Na san sirrin gwamnati - Osinbajo

Kwanaki aka rahoto Yemi Osinbajo ya na cewa da Buhari ya je ganin Likita a kasar waje, ya gano wasu abubuwan da babu wani wanda ya san da su a gwamnati.

Farfesa Osinbajo ya ce ya san Ubangiji ke bada mulki, amma yana ganin babu adalci a ce ya bar Aso Villa ya koma kauyensa ba tare da ya yi takara a 2023 ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel