Kusan 'yan takara a 2023: Jerin mutum 41 da ke hanyo gaje kujerar Buhari a zaben 2023

Kusan 'yan takara a 2023: Jerin mutum 41 da ke hanyo gaje kujerar Buhari a zaben 2023

A yayin da zaben shugaban kasa na 2023 ke gabatowa, ‘yan siyasa da dama daga jam’iyyu daban-daban na bayyana ra’ayinsu na hawa kujerar shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar Aso Rock Villa, Abuja.

An yi imanin cewa wasu mutane har yanzu suna saka yiwuwar ayyana aniyarsu, yayin da wasu wadanda ke ciki dumu-dumu, a halin yanzu ke neman goyon baya da shawarwari daga masu ruwa da tsaki da magoya baya.

A halin yanzu dai akwai akalla mutum 41 da ke son tsayawa takarar shugabancin kasar nan daga jam’iyyun siyasa kamarsu APC PDP, ADC, PRP, SDP, APGA, AP, da AAC.

Jerin 'yan takara daga jam'iyyun siyasar Najeriya
Kusan 'yan takarar 2023: Jerin masu hanyo gaje kujerar Buhari a zaben 2023 | Hoto: vox.com
Asali: UGC

Jerin sunayen ‘yan takara a jam’iyyun da aka ambata a sama sune kamar haka:

'Yan takara daga jam'iyyar APC

Kara karanta wannan

Ba a Taɓa Gwamnatin Da Ta Kai Ta Buhari Rashawa Ba: Naja'atu Mohammed Ta Ragargaji Buhari Kan Yafewa Dariya Da Nyame

  1. Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
  2. Prof Yemi Osinbajo
  3. Chief Rotimi Amaechi
  4. Dr. Chris Ngige
  5. Governor Yahaya Bello
  6. Ibinabo Joy Dokubo
  7. Ihechukwu Dallas-Chima
  8. Senator Orji Uzor Kalu
  9. Engr Dave Umahi
  10. Rev Moses Ayom
  11. Senator Rochas Okorocha
  12. Gbenga Olawepo-Hashim
  13. Ibrahim Bello Dauda
  14. Dr. Tunde Bakare
  15. Tein Jack-Rich

Daga jam'iyyar PDP

  1. Senator Bukola Saraki
  2. Senator Anyim Pius Anyim
  3. Peter Obi
  4. Alhaji Atiku Abubakar
  5. Dr Nwachukwu Anakwenze
  6. Sam Ohuabunwa
  7. Olivia Diana Teriela
  8. Dele Momodu
  9. Ayo Fayose
  10. Muhammed Hayatu-Deen
  11. Senator Bala Mohammed
  12. Alhaji Aminu Tambuwal
  13. Udom Emmanuel
  14. Nyesom Wike
  15. Chief Charlie Ugwu

Daga jam'iyyar ADC

  1. Prof Kingsley Moghalu
  2. Chukwuka Monye
  3. Dr. Mani Ibrahim
  4. SDP
  5. Adewole Adebajo
  6. Khadijah Okunnu-Lamidi
  7. PRP
  8. Patience Key
  9. Chief Kola Abiola

Jam'iyyar APGA

  1. Angela Johnson

Jam'iyyar AP

  1. Professor Christopher Imunolen

Jam'iyyar AAC

  1. Omoyele Sowore

Madam Nonye Josephine Ezeanyaeche

Kara karanta wannan

2023: APC ta rasa wani babban jigonta a jihar Oyo, ya sauya sheka zuwa PDP

2023: Hadimin Shugaban Kasa ya koma gida, zai shiga takarar ‘Dan Majalisa a Kano

A wani labarin, mai taimakawa shugaba Muhammadu Buhari a kafofin sada zumunta na zamani, Bashir Ahmaad ya na shirin takarar ‘dan majalisa a zaben 2023.

Malam Bashir Ahmaad ya bayyana haka a shafinsa na Facebook a ranar Talata. Ahmaad zai nemi kujerar Gaya/Ajingi/Albasu a majalisar wakilan tarayya.

Da yake bayani a shafin na sa, hadimin shugaban kasar ya tabbatar da cewa ya ziyarci mahaifarsa watau Gaya da ke wajen birnin Kano a cikin makon nan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.