Kusan 'yan takara a 2023: Jerin mutum 41 da ke hanyo gaje kujerar Buhari a zaben 2023
A yayin da zaben shugaban kasa na 2023 ke gabatowa, ‘yan siyasa da dama daga jam’iyyu daban-daban na bayyana ra’ayinsu na hawa kujerar shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar Aso Rock Villa, Abuja.
An yi imanin cewa wasu mutane har yanzu suna saka yiwuwar ayyana aniyarsu, yayin da wasu wadanda ke ciki dumu-dumu, a halin yanzu ke neman goyon baya da shawarwari daga masu ruwa da tsaki da magoya baya.
A halin yanzu dai akwai akalla mutum 41 da ke son tsayawa takarar shugabancin kasar nan daga jam’iyyun siyasa kamarsu APC PDP, ADC, PRP, SDP, APGA, AP, da AAC.

Asali: UGC
Jerin sunayen ‘yan takara a jam’iyyun da aka ambata a sama sune kamar haka:
'Yan takara daga jam'iyyar APC

Kara karanta wannan
Ba a Taɓa Gwamnatin Da Ta Kai Ta Buhari Rashawa Ba: Naja'atu Mohammed Ta Ragargaji Buhari Kan Yafewa Dariya Da Nyame
- Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
- Prof Yemi Osinbajo
- Chief Rotimi Amaechi
- Dr. Chris Ngige
- Governor Yahaya Bello
- Ibinabo Joy Dokubo
- Ihechukwu Dallas-Chima
- Senator Orji Uzor Kalu
- Engr Dave Umahi
- Rev Moses Ayom
- Senator Rochas Okorocha
- Gbenga Olawepo-Hashim
- Ibrahim Bello Dauda
- Dr. Tunde Bakare
- Tein Jack-Rich
Daga jam'iyyar PDP
- Senator Bukola Saraki
- Senator Anyim Pius Anyim
- Peter Obi
- Alhaji Atiku Abubakar
- Dr Nwachukwu Anakwenze
- Sam Ohuabunwa
- Olivia Diana Teriela
- Dele Momodu
- Ayo Fayose
- Muhammed Hayatu-Deen
- Senator Bala Mohammed
- Alhaji Aminu Tambuwal
- Udom Emmanuel
- Nyesom Wike
- Chief Charlie Ugwu
Daga jam'iyyar ADC
- Prof Kingsley Moghalu
- Chukwuka Monye
- Dr. Mani Ibrahim
- SDP
- Adewole Adebajo
- Khadijah Okunnu-Lamidi
- PRP
- Patience Key
- Chief Kola Abiola
Jam'iyyar APGA
- Angela Johnson
Jam'iyyar AP
- Professor Christopher Imunolen
Jam'iyyar AAC
- Omoyele Sowore
Madam Nonye Josephine Ezeanyaeche
2023: Hadimin Shugaban Kasa ya koma gida, zai shiga takarar ‘Dan Majalisa a Kano
A wani labarin, mai taimakawa shugaba Muhammadu Buhari a kafofin sada zumunta na zamani, Bashir Ahmaad ya na shirin takarar ‘dan majalisa a zaben 2023.
Malam Bashir Ahmaad ya bayyana haka a shafinsa na Facebook a ranar Talata. Ahmaad zai nemi kujerar Gaya/Ajingi/Albasu a majalisar wakilan tarayya.
Da yake bayani a shafin na sa, hadimin shugaban kasar ya tabbatar da cewa ya ziyarci mahaifarsa watau Gaya da ke wajen birnin Kano a cikin makon nan.
Asali: Legit.ng