Jam'iyyar PDP ta lallasa APC, ta lashe zaben Ciyamomi 21 da Kansiloli 226 a jihar Adamawa

Jam'iyyar PDP ta lallasa APC, ta lashe zaben Ciyamomi 21 da Kansiloli 226 a jihar Adamawa

  • Jam'iyyar PDP mai mulkin jihar Adamawa a arewa maso gabashin Najeriya ta cigaba da jan zarenta a zaɓen kananan hukumomi
  • Jam'iyya mai mulki ta lallasa abokiyar hamayyarta APC, ta lashe dukkan kujerun Ciyamomi 21 da kuma Kansiloli 226
  • APC ta yi watsi da sakamakon zaben da cewa ba'a gudanar da zaɓe ba, wasu ne kawai suka rubuta abinda ke ransu

Adamawa - Jam'iyyar PDP ta lashe baki ɗaya kujerun Ciyamomi da Kansiloli a faɗin kananan hukumomi 21 na jihar, kamar yadda Leadership ta rahoto.

Jam'iyyun siyasa da ba su gaza 18 ba ne suka tsayar da yan takara a zaɓen kananan hukumomin wanda aka gudanar ranar Asabar.

Da yake sanar da sakamakon zaɓen ranar Lahadi a Yola, babban birnin jihar Adamawa, shugaban hukumar zaɓen jiha mai zaman kanta (ADSIEC), Mr. Isa Shettima, ya ce APC da PDP ne kawai suka ɓarje gumi a zaɓen ciyamomi.

Kara karanta wannan

2023: Tinubu, Amaechi da wasu jiga-jigan APC 4 da Osinbajo zai gwabza da su ya gaji Buhari

Jam'iyyar PDP ta lallasa APC a Adamawa
Jam'iyyar PDP ta lallasa APC, ta lashe zaben Ciyamomi 21 da Kansiloli 226 a jihar Adamawa Hoto: leadership.ng
Asali: UGC

Shettima ya ce:

"Daga cikin jam'iyyu 18 da suka nuna sha'awa, Jam'iyyar PDP da APC ne kawai suka gwabza a zaɓen shugabannin kananan hukumomi."

Ya APC ta ji wannan shan ƙasa da ta yi?

Kakakin APC-Adamawa, Abdullahi Mohammed, da aka tuntuɓe shi, ya bayyana cewa babu wani zaɓen da aka gudanar a jihar, domin ba'a kai kayan zabe wasu runfuna na ba sam.

Ya ce a APC na cigaba da tattara kwararan shedun aikata maguɗi a zaɓen kuma zata sanar da matsayarta ba da jimawa ba, kamar yadda The cable ta rahoto.

Ya ce:

"Ba wani zaɓe da aka gudanar a baki ɗaya yankunan kananan hukumomi 21 dake faɗin jihar. Wasu tsirarun jami'an gwamnati ne suka zauna suka tsara sakamakon da ransu ke so."

Kara karanta wannan

Ku sake ba APC dama a 2023 mun ɗauki alkawari, Ahmad Lawan ya roki yan Najeriya

"APC ba zata yi ƙasa a guiwa ba, zata cigaba da harhaɗa kwararan shedu, ba da jimawa ba kowa zai ji matsayarta."

A wani labarin kuma Hotunan Katafariyar Gada Mai Hawa Uku da Ganduje Ke Ginawa a Kano, Babu Irinta a Faɗin Najeriya

Gwamnatin Kano na cigaba da aikin gada mai hawa uku a Shataletalen NNPC dake Anguwar Hotoro.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ce suna sa ran kammala aikin zuwa watan Satumba, an raɗa wa Gadar 'Muhammadu Buhari Interchange.'

Asali: Legit.ng

Online view pixel