Bidiyon Sanata Abdullahi Adamu yayin da ya isa fadar shugaban kasa domin ganawa da Buhari

Bidiyon Sanata Abdullahi Adamu yayin da ya isa fadar shugaban kasa domin ganawa da Buhari

  • Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya isa fadar shugaban kasa domin saka labule da Shugaban kasa Muhammadu Buhari
  • Sanata Adamu wanda wannan ne karo na farko da suke ganawa da shugaban kasar tun bayan da ya kama aiki a matsayin shugaban APC ya samu rakiyar Gwamna Mala Buni
  • Hadimin shugaban kasa, Bashir Ahmad ne ya sanar da labarin ganawar tasu a wata sanarwa da ya saki a yau Alhamis, 7 ga watan Afrilu

Fadar shugaban kasa, Abuja - A yanzu haka, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shiga cikin wata ganawar sirri da shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, Sanata Abdullahi Adamu.

Wannan shine karo na farko da Sanata Adamu ke ganawa da shugaban kasar tun bayan da ya kama aiki a matsayin shugaban jam’iyyar mai mulki na kasa a yan makonni da suka gabata.

Kara karanta wannan

Neman kujerar Shugaban kasa ya barka Atiku, Saraki da ‘Yan takarar PDP, kai ya rabu 3

Badiyon Sanata Abdullahi Adamu yayin da ya isa fadar shugaban kasa domin ganawa da Buhari
Badiyon Sanata Abdullahi Adamu yayin da ya isa fadar shugaban kasa domin ganawa da Buhari Hoto: @NigeriaGov
Asali: Twitter

Mai ba shugaban kasa shawara a shafukan sadarwa ta zamani, Bashir Ahmad ne ya sanar da batun ganawar tasu a cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na Twitter.

Sanata Adamu ya samu rakiyar Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe zuwa ganin shugaban kasar a fadar gwamnati da ke babbar birnin tarayya, Abuja.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ya rubuta a shafin nasa:

“Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu wanda ya samu rakiyar wanda ya gada, Mai girma Gwamna Mai Mala Bunin a jihar Yobe sun isa fadar shugaban kasa domin ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari, ganawarsu ta farko da shugaban kasar tun bayan da ya kama aiki a makonni da suka gabata.”

Gwamna Buni ya miƙa ragamar jam'iyyar APC hannun sabon shugaba na ƙasa

A gefe guda, mun kawo a baya cewa sabon shugaban jam'iyyar APC ta ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya karbi jagorancin jam'iyya ta ƙasa daga hannun shugaban riko.

Kara karanta wannan

Sau uku Ubangiji na kirana, ya ce Atiku ne zai gaji Buhari a 2023, inji Dino Malaye

Shugaban kwamitin rikon kwarya da shirya babban taro kuma gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, ya damƙa ragamar APC a hannun Adamu a hukumance.

Hakan ya kawo ƙarshen tsawon watanni 21 da Buni ya jagoranci APC tun bayan naɗa shi shugaban kwamitin riko.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng