Yanzu-Yanzu: Tsohon Shugaba a Majalisar Tarayya Ya Fice Daga APC, Ya Shiga Wata Jam'iyyar

Yanzu-Yanzu: Tsohon Shugaba a Majalisar Tarayya Ya Fice Daga APC, Ya Shiga Wata Jam'iyyar

  • Jam'iyyar APC mai mulkin kasa, a ranar Alhamis 7 ga watan Afrilu ta yi rashin daya daga cikin jiga-jigan yayanta, Lasun Yussuf, ya koma Labour Party
  • Yussuf wanda ya yi bikin komawarsa jam'iyyar Labour Party a Osun a ranar Alhamis, tsohon mataimakin kakakin majalisar dokokin tarayya ne
  • Tsohon dan majalisar zai fafata tare da wasu yan takarar a ranar 16 ga watan Yuli a lokacin da za a gudanar da zaben gwamnan Jihar Osun

Osogbo, Osun - Rt Honorabul Lasun Yussuf, tsohon mataimakin kakakin majalisar dokoki na tarayya, a ranar Alhamis, 7 ga watan Afrilu, ya koma jam'iyyar Labour Party, LP, a hukumance.

Yussuf ya sanar da komawarsa jam'iyyar ta LP a fili a ranar Alhamis a Osogbo, babban birnin Jihar Osun, kamar yadda New Telegraph ta rahoto.

Kara karanta wannan

Tsohon Minista Ya Dawo PDP Bayan Shekaru 8 a APGA, Zai Yi Takarar Gwamna a 2023

Yanzu-Yanzu: Tsohon Shugaba a Majalisar Tarayya Ya Fice Daga APC, Ya Shiga Wata Jam'iyyar
Tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Tarayya Ya Fice Daga APC, Ya Shiga Wata Jam'iyyar. (Photo: I Support Hon Lasun Yusuf)
Asali: Facebook

Yana sa ran zai yi takarar kujerar gwamna ne a jihar wacce za a yi zaben a ranar 16 ga watan Yuli.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Tsohon dan majalisar, a baya-bayan nan ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar All Progressives Congress, APC, mai mulkin kasa.

Hadimin El-Rufai Ya Koma Jam'iyyar PDP, Zai Yi Takarar Gwamna a 2023

Jimi Lawal, Mashawarci na muamman ga gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan habbaka saka hannun jari, ya shiga jam'iyyar PDP a Jihar Ogun., rahoton Daily Trust.

Lawal, wanda ya ziyarci sakatariyar PDP a Abeokuta, ranar Asabar, ya kuma ayyana niyarsa na yin takarar gwamna a zabe da ke tafe.

Ma'aikacin bankin da ya samu horaswa a Landan ya nemi kujerar gwamna a karkashin APC a zaben 2019, amma ya sha kaye hannun Gwamna Dapo Abiodun.

Kara karanta wannan

PDP da APC sun yi babban rashi: Tsohon Sanata, tsaffin yan majalisa, mambobi 10,000 sun koma NNPP

Tsohon Minista Ya Dawo PDP Bayan Shekaru 8 a APGA, Zai Yi Takarar Gwamna a 2023

A bangare guda, Tsohon ministan labarai, Labaran Maku, ya dawo jam'iyyar PDP, don fafatawa a takarar gwamnan Jihar Nasarawa da gwamna mai ci yanzu Abdullahi Sule a babban zaben 2023, rahoton The Punch.

Maku ya dawo jam'iyyar PDP bayan shafe shekaru takwas a APGA, inda ya rike mukamin sakataren jam'iyyar na kasa kafin ficewarsa.

Da ya ke magana a ranar Laraba a mazabarsa ta Wakama, karamar hukumar Nasarawa-Eggon a jihar, tsohon ministan ya ce ya koma PDP ne saboda magoya bayansa sun bukaci hakan.

Asali: Legit.ng

Online view pixel