2023: Tambuwal da Peter Obi za su shiga labule da masu ruwa da tsaki na PDP a majalisar tarayya a yau

2023: Tambuwal da Peter Obi za su shiga labule da masu ruwa da tsaki na PDP a majalisar tarayya a yau

  • Za a saka labule tsakanin Gwamna Aminu Tambuwal, Peter Obi da kuma mambobin PDP a majalisar dokokin tarayya
  • Ana sanya ran jiga-jigan na PDP za su gana ne a daren yau Talata, 5 ga watan Afrilu, da misalin karfe 9:00
  • Tuni masu neman takarar shugabancin kasar biyu suka aike da wasika kan haka zuwa zauren majalisar wakilai, wanda Gbajabiyamila ya karanto a yayin zamansu

Abuja - Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal da tsohon gwamnan jihar Anambra, za su gana da mambobin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a majalisar dokokin tarayya a yau Talata, 5 ga watan Afrilu.

Kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila, ne ya karanto wasikar Tambuwal da Obi wanda a ciki ne suka gabatar da bukatar tasu ta son zantawa da yan majalisar na PDP, a zauren majalisa.

Kara karanta wannan

Neman kujerar Shugaban kasa ya barka Atiku, Saraki da ‘Yan takarar PDP, kai ya rabu 3

Wasikar na dauke da sa hannun Ndudi Elumelu, shugaban marasa rinjaye a majalisar wakilan, jaridar The Cable ta rahoto.

2023: Tambuwal da Peter Obi za su shiga labule da masu ruwa da tsaki na PDP a majalisar tarayya a yau
2023: Tambuwal da Peter Obi za su shiga labule da masu ruwa da tsaki na PDP a majalisar tarayya a yau Hoto: Premium Times
Asali: UGC

Rahoton ya kuma nuna cewa za a yi taron ne da misalin karfe 9:00 na daren yau kuma zai gudana ne a Wuse 2 da ke Abuja.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Bayan karanto wasikar, sai Gbajabiamila ya tambayi shugaban marasa rinjayen ko Tambuwal da Obi za su hade ne don yin takarar shugaban kasa a tare.

Da yake martani, Elumelu ya ce:

“Siyasa ce ba da gaba ba kamar yarjejeniyarku na Eagle Square."

Yayin da Obi ya ayyana aniyarsa ta takarar shugabancin kasar a 2023 a ranar 24 ga watan Maris, har yanzu Tambuwal na kan tuntuba ne kuma bai ayyana kudirinsa ba tukuna.

2023: Atiku, Wike da sauransu za su san makomarsu a yau yayin da kwamitin shiyya na PDP zai zartar da hukunci

Kara karanta wannan

Buhari ya nemi Sanatoci su tabbatar da sababbin mukamai 5 da ya nada a hukumomin gwamnati

A wani labarin, mun ji cewa ana sanya ran kwamitin rabon mukaman shugabanci na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) mai mambobi 37 zai sanar da hukuncinsa kan tsarin rabon shiyya-shiyya na jam’iyyar a zaben shugaban kasa na 2023.

Kwamitin ya shirya yin watsi da tsarin karba-karba na jam’iyyar domin ba masu takarar shugaban kasarta damar fafatawa don mallakar tikitin jam’iyyar a zaben fidda gwani da za a yi a ranakun 28-29 ga watan Mayu.

Masu takarar kujerar shugaban kasa suna ta tuntuba da kamun kafa domin tabbatar da ganin cewa hukuncin da kwamitin zai dauka bai kawo masu cikas ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng