APC Ta Yi Rashi Yayinda Ƙanin Gwamna, Buhari, Da Wasu Mutane Da Dama Suka Koma PDP

APC Ta Yi Rashi Yayinda Ƙanin Gwamna, Buhari, Da Wasu Mutane Da Dama Suka Koma PDP

  • Jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP, ta kara karfi a Jihar Niger a yayin da ta karbi sabbin mambobi da suka baro APC
  • Aminu, kanin Gwamna Abubakar Sani Bello, Abubakar Buhari da wasu da dama sun fice daga APC gabanin zaben shekarar 2023
  • Shugaban jam'iyyar PDP na mazabar Kontagora Central, Umar Hassan, ne ya karbi sabbin mambobin, ya kuma basu katinsu na PDP

Niger - Wasu dandazon mutane sun sake ficewa daga jam'iyyar All Progressives Congress, APC a jihar Niger sun koma PDP cikinsu har da Gwamna Abubakar Sani Bello.

Kanin Bello, Aminu, shahararren dan siyasa a Niger North, Abubakar Buhari da wasu da dama sun fice daga APC sun koma babban jam'iyyar adawa.

APC Ta Yi Rashi Yayinda Ƙanin Gwamna, Buhari, Da Wasu Mutane Da Dama Suka Koma PDP
APC Ta Yi Rashi Yayinda Wasu Jiga-Jiganta Suka Fice Suka Koma PDP. Photo credit: @chiefpressngs
Asali: Twitter

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kara karanta wannan

Ko PDP ta so, ko ta ki, sai APC ta lashe zaben 2023: Mataimakin Shugaban Majalisar dattawa

Sabbin wadanda suka sauya shekan, a cewar wani rahoto da New Telegraph ta wallafa, sun karbi katinsu na zama mambobin PDP daga hannun shugaban jam'iyyar na mazabar Kontgora Central, Umar Hassan.

An gano cewa kanin gwamnan, Aliyu daga Kontagora Central da Buhari sun karbi katinsu na zama yan jam'iyyar PDP.

Yahaya Abdullahi Ability, shugaban yankin Niger North, ya yi maraba da mutanen biyu da suka dawo PDP. A jawabinsa, Ability, ya bukaci su jajirce don ganin PDP ta yi nasara.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164