Sunayen Manyan Jami'an Sojin Najeriya da Suka Mutu a Bakin Aiki daga 2016 zuwa 2026
- Daga shekarar 2016 zuwa 2026, rundunar sojojin Najeriya ta rasa wasu manya manyan jami'an soji a dai dai lokacin da suke fafatawa da 'yan ta'adda
- A 2016, rundunar ta girgiza da mutuwar Laftanal Kanal Muhammad Abu Ali, wanda 'yan ta'addar Boko Haram suka kashe a garin Malam Fatori
- A kwanan nan, an samu labarin kisan Birgediya Janar O. Braimah a Benisheikh; lamarin da ya sa Legit Hausa ta jero manyan sojojin da aka kashe
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Borno - Tarihin yaƙi da ta’addanci a Najeriya, musamman a yankin Arewa maso Gabas, ya nuna yadda manyan jami'an sojojoji suka sadaukar da rayuwarsu a fagen daga.
Ɗaya daga cikin rashin da ya fi girgiza ƙasa shi ne kisan Laftanal Kanal Muhammad Abu Ali a ranar 4 ga Nuwamba, 2016, a garin Malam Fatori.

Source: Getty Images
Kisan Kanal Abu Ali da Kanal Dahiru Bako
Kamar yadda jaridar Premium Times ta ruwaito, Abu Ali ya kasance babban jami’i dake jagorantar bataliya ta 272, kuma an yaba masa matuƙa wajen ƙwato garuruwa da dama daga hannun Boko Haram kafin ajali ya cimmasa a wani harin kwanton ɓauna.
Bayan wannan rashi, rundunar sojojin Najeriya ta ci gaba da fuskantar ƙalubale inda wasu manyan jami’ai suka amsa kiran mahalicci a yayin da suke a fagen daga.
A watan Satumban 2020, Kanal Dahiru Chiroma Bako ya rasu sakamakon raunukan da ya ji bayan dakarunsa sun fuskanci harin kwanton ɓauna a kusa da Damboa.
Rahoton Daily Trust ya nuna cewa Bako ya shahara wajen jajircewa a yaƙin da ake yi a dajin Sambisa, kuma har shugaban kasa a wancan lokacin ya bayyana shi a matsayin gwarzon soja da ba ya tsoron mutuwa.
Kisan janar-janar din sojojin Najeriya
Mafi girman rashi a matakin janar-janar ya faru ne a ranar 13 ga Nuwamba, 2021, lokacin da aka kashe Birgediya Janar Dzarma Zirkusu a garin Askira Uba dake Jihar Borno.
Kamar yadda kafar yaɗa labarai ta BBC Hausa ta tabbatar, Zirkusu shi ne babban jami’i mafi girman matsayi da aka taɓa kashewa a fagen fama a wancan lokacin.
Ya rasa ransa ne yayin da yake jagorantar dakarunsa don fatattakar mayakan ISWAP da suka kai farmaki garin, wanda hakan ya sa aka karrama shi a matsayin babban jarumin ƙasa.
A cikin shekarun baya-bayan nan na 2025 zuwa 2026, jerin jaruman ya ƙara tsayi da kisan Birgediya Janar M. Uba a ƙarshen shekarar 2025 da kuma na baya-bayan nan, Birgediya Janar O. Braimah, wanda aka kashe a ranar 9 ga Afrilu, 2026, a yankin Benisheikh.
Rahoton jaridar The Cable ya bayyana cewa waɗannan jami’an sun mutu ne yayin gudanar da samamen sintiri da nufin tabbatar da tsaron hanyar Maiduguri zuwa Damaturu.
Jerin sunayen manyan jami'an da aka kashe

Source: Getty Images
Ga cikakken jerin manyan sojojin Najeriya da aka kashe a fagen daga, daga shekarar 2016 zuwa 2026, kamar yadda StatiSense ta wallafa a shafinta na X.

Kara karanta wannan
An yi rashi: Yadda 'yan ta'addan ISWAP suka kashe babban Janar da sojoji 17 a Borno
Shekara | Rana | Suna da matsayi | Wurin da kisan ya faru |
2016 | 16 Oktoba | Laftanal Kanal K. Yusuf | Asaga, Jihar Borno |
2016 | 04 Nuwamba | Laftanal Kanal Muhammad Abu-Ali | Malam Fatori, Jihar Borno |
2016 | 15 Nuwamba | Laftanal Kanal B. U. Umar | Hanyar Bitta-Pirang, Adamawa |
2016 | 12 Disamba | Laftanal Kanal O. Umusu | Gudumbali, Jihar Borno |
2018 | 18 Nuwamba | Laftanal Kanal Ibrahim Sakaba | Arewacin Jihar Borno |
2020 | 21 Satumba | Kanal Dahiru Chiroma Bako | Damboa (Wajirko), Borno |
2020 | 24 Satumba | Laftanal Kanal M. Z. Manu | Jihar Katsina |
2021 | 13 Nuwamba | Birgediya Janar Dzarma Zirkusu | Askira Uba, Jihar Borno |
2025 | 17 Nuwamba | Birgediya Janar M. Uba | Kusa da Wajiroko, Borno |
2026 | 09 Afrilu | Birgediya Janar O. Braimah | Benisheikh, Jihar Borno |
Martanin Tinubu kan kisan Janar Braimah
A wani labari, mun ruwaito cewa, Shugaba Bola Tinubu ya sha alwashin murkushe ta’addanci bayan harin da ya kashe Birgediya Janar O. Braimah a jihar Borno.
Shugaban ya bayyana haka ne bayan sojoji sun dakile farmakin ‘yan Boko Haram a Benisheikh, amma an yi asarar rayuka da dama.
Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa rashin babban jami'in sojin ba zai sare ayyukan rundunar sojin kasar nan ba wajen yakar yan ta'adda.
Asali: Legit.ng

