NiMet: Za a Sheka Ruwan Sama a Kaduna, Taraba da Wasu Jihohi a Ranar Laraba
- Hukumar NiMet ta yi hasashen cewa za a samu ruwan sama da tsawa a wasu jihohin Arewa da Kudu a safiya da yammacin ranar Laraba
- Kudancin Najeriya ne zai samu ruwan sama mai yawa, inda ruwan zai sauka a kusan dukkan jihohin shiyyar, a cewar rahoton NiMet
- NiMet ta gargadi masu fama da cututtukan numfashi da su takaita zirga-zirga waje, sannan direbobi su yi taka tsantsan da yayin da ake ruwa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja – Hukumar da ke kula da hasashen yanayi ta Najeriya, watau NiMet, ta fitar da hasashen yanayin da za a tashi da shi a gobe Laraba, 8 ga Afrilu, 2026.
NiMet ta yi hasashen cewa za a samu yanayin kura da hazo a wasu sassan ƙasar, yayin da wasu sassan za su fuskanci ruwan sama da iska.

Source: Original
Hasashen yanayi a wasu jihohin Arewa
Wannan na kunshe ne a cikin rahoton hasashen yanayi da NiMet ta fitar a shafinta na X a yammacin ranar Talata, 7 ga watan Afrilu, 2026.
A safiyar Laraba, ana sa ran cewa za a samu samu matsakaiciyar iska mai dauke da kura wadda za ta iya rage hangen nesa ga matafiya a jihohin Borno, Yobe, Kano, Katsina, Zamfara, Jigawa, Kebbi, da Sokoto.
Da yamma kuwa, za a iya samun ruwan sama hade da tsawa a wasu sassan jihohin Taraba, Bauchi, Kaduna, Adamawa, da Gombe yau.
Idan aka leka Arewa ta tsakiya kuwa, NiMet ta yi hasashen cewa za a samu hadari, amma rana za ta fito tangaran, a jihohin Neja, Kwara, da Kogi.
Idan yamma ta yi kuma, ana hasashen samun ruwan sama zai sauka a jihohin Nasarawa, Plateau, Kwara, Kogi, Benue, har ma da babban birnin tarayya Abuja.
Hasashen yanayin ruwa a jihohin Kudu
Hasashen NiMet ya nuna cewa za a samu haduwar hadari da kuma saukar ruwan sama da tare da tsawa a jihohin Oyo, Osun, Ekiti, Ogun, Ondo, Edo, Legas, Cross River, Akwa Ibom, Bayelsa, Rivers, da Delta.
Da yammacin ranar ta Laraba, ruwan sama da tsawa za su karu a daukacin yankin Kudu, wanda hakan zai janyo santsin titi da kuma rage gani ga matafiya, a cewar NiMet.

Source: Twitter
Shawarwarin NiMet ga 'yan Najeriya
Hukumar NiMet ta ba da waɗannan shawarwari domin kiyaye kai yau:
- Kura na iya shafar masu ciwon 'asama' ko sauran matsalolin numfashi, don haka mutane su rage fita waje.
- Iska mai ƙarfi na iya kaɗawa kafin ruwa ya fara, don haka a tabbatar an killace abubuwan da iska kan iya ɗauka.
- Direbobi su rage gudu saboda rashin gani da kuma santsin titi, don guje wa afkuwar hadurra.
- A guji shiga wuraren da ruwa ke yawan taruwa ko yake wucewa da karfi yayin da ake ruwan sama.
- Kamfanonin jiragen sama su nemi cikakken rahoton yanayi daga NiMet kafin su tsara tashi ko saukar jiragensu.
Karanta hasashen yanayin a nan kasa:
Hasashen rana da ruwa a Najeriya
A wani labarin, Legit Hausa ta rahoto cewa NiMet ta yi hasashen cewa jihohin Arewa za su fuskanci zafi da rana tare da yiwuwar tsawa da ruwan sama.
A bisa hasashen hukumar a jihohin Arewa ta Tsakiya, ana sa ran samun ruwan sama tun da sanyin safiya sannan a samu rana daga baya.
A Kudu kuwa, NiMet ta ce za su fuskanci ruwan sama mai yawa wanda ka iya haddasa cunkoso da jinkirin zirga-zirga abubuwan hawa.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


