Harin Bam a Borno: Sanata Ndume Ya Faɗawa Tinubu abin da Ya Kamata Ya Yi
- Sanata Ali Ndume ya fadawa Shugaba Bola Tinubu cewa tsaron rayukan 'yan Najeriya ya fi siyasar 2027 muhimmanci
- Ndume ya nemi Tinubu ya ziyarci Borno ko ya tura mataimakinsa domin jajanta wa iyalan mutane 25 da bam ya kashe
- Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya yi magana game da wadanda harin bama-bamai ya kashe a Maiduguri
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - Sanata Ali Ndume, ya yi kira ga gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da ta ba da fifiko ga batun tsaron ‘yan ƙasa maimakon maida hankali kan shirye-shiryen siyasar 2027.
Sanatan mai wakiltar Borno ta Kudu ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Abuja.

Source: Facebook
Sakon Sanata Ali Ndume ga Tinubu
Ali Ndume ya nuna damuwarsa kan yadda rayukan mutane ke salwanta a yankin Arewa maso Gabas da sauran sassan ƙasar, kamar yadda rahoton Vanguard ya nuna.
Sanatan ya jaddada cewa "masu fita su kaɗa ƙuri'a na mutuwa kullum," don haka ya bukaci shugaban ƙasa da ya dauki mataki, a gani a ƙasa, ba wai ya tsaya a maganganu kawai ba.
Ya bayyana cewa har yanzu akwai mutane da dama da ba a gan su ba tun bayan kisan kiyashin da aka yi a Ngoshe, wannan ya ce abin takaici ne matuka.
Sannan Sanata Ndume ya bukaci gwamnatin tarayya da ta tabbata ta kamo waɗanda suka kai hare-haren bama-bamai na ranar Litinin a Maiduguri don hukunta su.
Shawarwarin Ndume ga gwamnatin tarayya
Sanata Ali Ndume ya ba da shawarar cewa idan Shugaba Tinubu ba zai iya ziyartar jihar Borno ba, to ya tura mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, domin ya tabbatar wa 'yan Najeriya cewa gwamnati na damuwa da halin da suke ciki.
Ya kuma bukaci a daina nuna halin ko-o-ho ga matsanancin rashin tsaro da ƙasa ke ciki, inda ya ce babban nauyin kowace gwamnati shi ne kare rayuka da dukiyoyin al'umma.
Shettima ya magantu kan harin Borno

Source: Twitter
A gefe guda kuma, Kashim Shettima ya bayyana alhininsa kan rasuwar mutane 25 da suka rasa rayukansu a hare-haren bama-baman na Maiduguri.
Shettima ya yi wannan jawabi ne a ranar Talata yayin rufe karatun Tafsirin Ramadan na shekara-shekara a masallacin fadar shugaban ƙasa dake Abuja, in ji rahoton Punch.
Mataimakin shugaban ya jaddada cewa babu wani addini da ya amince da kashe rayukan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, inda ya yi addu'ar Allah ya jikan waɗanda suka rasu.
Tinubu ya yi magana kan harin Borno
A wani labari, mun ruwaito cewa, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi magana game da hare-haren 'yan kunar bakin wake da aka kai Maiduguri.
Shugaba Tinubu ya kara da cewa 'yan ta'addan suna kai hare-haren ne saboda yadda jami'an tsaro suka matsa musu lamba a dazuka.
Shugaban kasar ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta cigaba da daukar matakan da suka dace domin magance barazanar 'yan ta'adda a kasar nan.
Asali: Legit.ng

