Azumi Ya Zo Karshe, Sarkin Musulmi Ya Fitar Sanarwa kan Ranar Karamar Sallah a Najeriya
- Sarkin Musulmin Najeriya, Muhammad Sa'ad Abubakar III ya bukaci a fara duban jinjirin watan Shawwal daga gobe Laraba, 29 ga Ramadan, 1447AH
- Ya bukaci duk wanda ya ga watan ya sanar da Hakimi ko Mai Unguwa mafi kusa da shi domin isar da sakon ga fadar Sarkin Musulmi
- Idan aka ga watan a gobe Laraba, hakan na nufin za a yi karamar Sallah ranar Alhamis, amma idan ba a gani ba, sallah za ta kama ranar Juma'a
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Sokoto, Nigeria - Mai alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya (NCIA), Muhammad Sa'ad Abubakar III, ya nemi a fara duban watan Karamar Sallah.
Sultan ya bukaci al’ummar Musulmi a fadin Nigeria da su fara neman jinjirin watan Shawwal wanda zai nuna karshen watan azumin Ramadan da kuma ranar hawa idin Karamar Sallah.

Kara karanta wannan
Duk da ba ya Najeriya, Zulum ya aiko da sako bayan tagwayen bama bamai a Maiduguri

Source: Facebook
Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmin ta wallafa a shafinta na Facebook, yau Talata, 28 ga watan Ramadan, 1447AH daidai da 17 ga watan Maris, 2026.
Ranar fara duban watan Sallah a Najeriya
Sanarwar wacce Sambo Wali Junaidu, Wazirin Sakkwato kuma shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin addini, ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa za a fara duban watan ne ranar Laraba.
Sanarwar ta ce:
“Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Musulunci ta Najeriya, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, CFR, mni, na kira ga Musulmi a fadin kasar nan da su nemi jinjirin watan Shawwal a ranar Laraba, 18 ga Maris, 2026."
Yadda mutum zai kai sakon ganin wata
Ta kara da cewa duk Musulmin da ya ga jinjirin watan ya kai rahoton ganin sa ga Hakimi ko Mai Unguwa mafi kusa da shi, domin isar da sakon ga Majalisar Sarkin Musulmi don tabbatarwa.
“Musulman da suka ga sabon watan su sanar da ga Hakimi ko Mai Unguwa mafi kusa, wanda shi kuma zai isar da wannan bayani ga Mai Alfarma Sarkin Musulmi, domin yin sanarwa ta gaba,” in ji sanarwar.

Source: Twitter
Lambobin da za a kira idan an ga wata
Fadar Sarkin Musulmi ta kuma bayar da wasu lambobin waya na musamman domin kai rahoton ganin jinjirin wata kai tsaye ga ofishin kwamitin ganin Mal.
Lambobin sun su ne: 0803 715 7100, 0806 630 3077, 0803 596 5322, 0803 594 5903, 0706 714 6900
Ganin jinjirin watan Shawwal, 1447 yana nufin karshen watan azumin Ramadan, da kuma fara bukukuwan Sallah Karama (Eid El-Fitr).
Za a fara duban watan Shawwal a Saudiyya
A wani labarin, kun ji cewa Saudiyya ta bukaci musulmi su fara duban jinjirin watan Shawwal daga yammacin ranar Laraba, 29 ga watan Ramadan, 1447AH.
A sanarwar da Saudiyya ta fitar, ta ce sakamakon duba jinjirin watan da za yi a ranar Laraba mai zuwa ne zai tabbatar da ranar idin karamar Sallah (Eid al‑Fitr).
Hukumomim Saudiyya sun kuma yi kira ga duk wanda ya ga jinjirin watan da idonsa ko ta hanyar na’ura, da ya garzaya kotu mafi kusa domin bada shaida.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
