Malamai Sun Nuna Kishi, Sun Goyi bayan 'Dan APC domin Samun Musulmin Gwamna

Malamai Sun Nuna Kishi, Sun Goyi bayan 'Dan APC domin Samun Musulmin Gwamna

  • Kungiyoyin Musulmi da na malamai a Osun sun bayyana goyon bayansu ga dan takarar APC yayin da ake shirin zaben gwamna
  • Shugaban kungiyar, Sheikh Qozeem Abdul Rahaman, ya ce Musulmi su mara wa Bola Tinubu baya tare da zaben Musulmi a matsayin gwamna domin ci gaba da manufofin gwamnati
  • Dan takarar ya ce ba zai dogara da karfin gwamnatin tarayya ba domin lashe zaben Osun, yana mai kira ga jama'a su karbi katin zabe

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Osogbo, Osun - Masu ruwa da tsaki da kungiyar malaman Musulunci a Osun sun tabbatar da goyon baya ga APC.

Ƙungiyar malaman ta bayyana goyon baya ga dan takarar APC, Asiwaju Bola Oyebamiji da mataimakinsa Benjamin Adereti.

Malamai sun goyi bayan dan takarar gwamna a APC
Taswirar jihar Osun da ake shirin zabe a 2026. Hoto: Legit.
Source: Original

Osun: Musulmi sun bi bayan dan takarar APC

Kara karanta wannan

'Yadda Shugaba Tinubu ya hana Trump kawo farmaki don mamaye Najeriya'

Sun bayyana hakan ne a wani taron Ramadan inda suka raba kayan abinci ga mabiya addini tare da kira ga jama'a su goyi bayan gwamnatin Bola Tinubu, cewar The Nation.

Shugaban kungiyar Musulmin, Sheikh Qozeem Abdul Rahaman, ya ce ya dace Musulmi su mayar da alherin da aka nuna musu ta hanyar mara wa Tinubu baya.

Ya kuma ce a duk jihohin Kudancin Najeriya 17 babu gwamnan Musulmi a yankin Kudu maso Yamma, yana cewa wannan lamari abin damuwa ne.

Malaman Musulunci sun goyi bayan Bola Tinubu

Sheikh Abdul Rahaman ya ce dole Musulmi su hada kai domin zaben gwamna Musulmi wanda zai taimaka wajen dorewar shirye-shiryen da gwamnatin Tinubu ta fara.

Malamin da ya gabatar da lacca, Farfesa Kamaldeen Busari, ya ce Oyebamiji ba musulmin bogi ba ne, kuma cikakken Musulmi ne mai sadaukarwa.

Ya kara da cewa zai zama abin takaici idan al'ummar Osun suka rasa wannan dama ta zabar Oyebamiji wanda ya bayyana a matsayin jagoran Musulmi nagari.

Malaman Musulunci sun goyi bayan dan takarar APC
Malamai Musulunci Yayin taro da Gwamna Ademola Adeleke a gidan gwamnatin Osun. Hoto: @aadeleke_01.
Source: Instagram

Martanin dan takarar APC a zaben Osun

Da yake mayar da martani, Oyebamiji ya ce ba zai dogara da karfin gwamnatin tarayya ba wajen lashe zaben gwamnan Osun na shekarar 2026.

Kara karanta wannan

Malamai sun yi magana, sun fadi yadda yakin Iran da Amurka ya shafi Najeriya

Ya ce jam'iyyar APC ta riga ta tuntubi dukkan kananan hukumomi 30 da ofishin yankuna tare da sarakunan gargajiya da mata da maza, cewar ThisDay.

Oyebamiji ya ce za su ci gaba da aiki tukuru domin samun damar zama gwamnan Osun, yana jaddada cewa dole su nuna kyakkyawan hali ga jama'a.

Ya kuma roki masu kada kuri'a su tabbatar sun karbi katin zabe na dindindin kafin lokacin zaben gwamna da za a gudanar a watan Agustan shekarar 2026 da muke ciki.

Kwara: Ana neman sauya gwamna da Kirista

Kun ji cewa Kungiyar Kwara Inclusion Advocates (KIA) ta sake kiran a samu gwamna Kirista a Kwara domin samar da adalci.

Ta ce tsarin mulki ya daɗe yana fifita bangare ɗaya wanda ke nuna rashin daidaito inda ta yi kiran samar da adalci gaba daya.

Kungiyar ta ja kunnen ‘yan siyasa su guji siyasar raba kawuna, tana cewa zaben 2027 zai nuna ko Kwara za ta rungumi adalci ko siyasar yaudara.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.