Magana Ta Kare: Kotu Ta Yanke Hukuncin Karshe a Shari'ar Abba Kyari da Gwamnati
- Babbar kotun tarayya ta wanke DCP Abba Kyari daga tuhume tuhume 23 da suka shafi kin bayyana kadarori da NDLEA ta shigar
- Mai shari'a James Omotosho ya bayyana cewa NDLEA ta gaza gabatar da kwararan shaidu domin tabbatar da zargin da take yi wa Kyari
- Har yanzu Kyari da wasu jami'an yan sanda hudu suna fuskantar wata shari'ar daban kan zargin safarar hodar iblis da wasu kwayoyi
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - Wata babbar kotun tarayya dake birnin Abuja ta yanke hukuncin karshe a shari'ar Abba Kyari, mataimakin kwamishinan yan sanda (DCP) da aka dakatar, da hukumar NDLEA.
Kotu ta wanke tare da sallamar Abba Kyari daga zarge-zarge 23 dake da alaka da kin bayyana kadarori, da NDLEA ta shigar a kansa da wasu 'yan uwansa.

Kara karanta wannan
El Rufai: ICPC ta fitar da jerin abubuwa 67 da ta samu a gidan tsohon gwamnan Kaduna

Source: Facebook
NDLEA: Kotu ta wanke Abba Kyari
Hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) ce ta shigar da karar tana zargin Kyari da boye wasu kadarori da ake zargin mallakinsa ne, in ji rahoton The Cable.
An gurfanar da Kyari ne tare da kannensa guda biyu, wadanda ake zargi da yin rantsuwar karya domin boye asalin wasu kaddarori da ake alakantawa da dan sandan.
Sai dai, a hukuncin da ya yanke yau Alhamis, Mai shari’a James Omotosho ya bayyana cewa masu kara sun gaza gabatar da kwararan hujjoji kan zargin da suke yi.
Yayin da yake karanta hukuncin, Mai shari’a Omotosho ya bayyana cewa NDLEA ba ta gabatar da gamsassun shaidu da hujjoji da za su nuna cewa kadarorin da aka ambata a cikin karar mallakar Abba Kyari ne ba.
Lauyoyin NDLEA sun gaza gabatar da hujjoji
Mai shari'ar ya yi bayanin cewa za a iya tabbatar da mallakar fili ne kawai ta hanyar tarihin gado, takardun mallaka, ko kuma shaidar mallakar filin, amma NDLEA ba ta gabatar da ko daya daga cikin wadannan shaidun ba.
Musamman kan gidan dake rukunin gidajen Fountain Estate dake Kasana, wanda ake zargin na Abba Kyari ne, kotu ta gano cewa na Ramatu Kyari ne, kuma babu wata hujja dake nuna cewa na d'an sandan ne.
Haka kuma, kotun ta gano cewa kadarorin dake Asokoro da Maiduguri babu shaidar dake alakanta su da Abba Kyari.
A yayin kare kansa, Abba Kyari ya shaida wa kotu cewa kadarorin dake jihar Borno na mahaifinsa ne wanda ya rasu, kuma gado ne shi da sauran yan uwansa suka raba.
Kotu ta nemi a daina gallazawa Kyari
Mai shari'a Omotosho ya bayyana cewa NDLEA ba ta iya karyata wannan ikirari na Kyari ba, kamar yadda Channels TV ta ruwaito.
Sannan kuma, kotun ta yi watsi da zargin hadin baki da ake yi wa kannen Kyari, Mohammed da Ali Kyari, inda ta bayyana zargin a matsayin wanda ba shi da tushe.
Mai shari'a ya siffanta karar ta NDLEA a matsayin mai rauni, yana mai cewa Abba Kyari ya yi wa kasa aiki don haka bai kamata a dinga gallaza masa ba muddin babu kwararan shaidun laifi.
Sai dai, har yanzu Kyari da wasu jami'an yan sanda hudu suna fuskantar wata shari'ar daban a gaban Mai shari'a Emeka Nwite kan zargin safarar hodar iblis.

Source: Facebook
Abin da lauyan Kyari ya ce
Bayan yanke hukuncin, daya daga cikin lauyoyin Abba Kyari, watau Hamza Nuhu Dantani, ya wallafa a shafinsa na Faebook cewa:
"Nasara daga Allah!! AlhamudulilLahi.
"Yau babbar kotun dake Abuja ta wanke duk tuhuma da NDLEA sukeyi Akan Abba Kyari.. akan Laifuffuka 23.
"Tace bai dace ace sun yi mashi irin wannan mummunan sharrin ba, a kan lamari na mallakar dukiyoyin da kuma almundahana..
"Kotu ta ce sun kasa gamsar da ita akan cewa Abba Kyari mai laifi ne.
"Kotu ta ce Abba Kyari, jajirtacen 'dan sanda ne, kuma haziki ne, bai dace a ce an saka mashi da wannan sharrin ba, a matsayinsa na mutumin da ya bada gudunmawarsa a harkar tsaro.
Hamza Nuhu Dantani ya ce saura daya shari'ar wadda take gaban wata kotun, kuma suna da yakin ita ma za su yi nasara.
Wasu kadarori da aka ce Kyari ya mallaka
Mun kawo muku labarin cewa Gwamnatin tarayya ta gano wasu kadarori 14 wanda ake zargin Abba Kyari ya mallaka na filaye, gidaje da makudan kudade.
Ofishin Ministan shari’a kuma babban Lauyan gwamnatin Najeriya yana zargin DCP Kyari da laifin boye gaskiya a game da mallakar wadannan dukiyoyi.
An shigar da karar mai lamba FHC/ABJ/CR/408/22 a kotun tarayya na garin Abuja. Mohammed Kyari da Ali Kyari suna cikin wadanda ake kara a shari'ar.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


