Kwana Ya Kare: Sarki Mai Martaba a Najeriya Ya Riga Mu Gidan Gaskiya a Watan Azumi
- A yau Litinin, 2 ga watan Maris, 2026, aka tabbatar da rasuwar Sarkin Ikire da ke jihar Osun, Oba Olatunde Falabi, yana dan shekara 91
- Shugabar karamar hukumar Irewole da ke jihar Osun, Dr Esther Okunola ta tabbatar da aukuwar lamarin, ta mika sakon ta'aziyya ga iyalan mamacin
- Ta ce al'ummar yankin masarautar sun yi rashin uba, wanda hikimarsa, jarumtarsa da shawarwarinsa suka kasance ginshikin hadin kan al'umma
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Osun, Nigeria - Sarkin Ikire da ke jihar Osun a Kudancin Najeriya, Oba Olatunde Falabi, ya riga mu gidan gakiya, yana da shekaru 91 a duniya.
Shugabar karamar hukumar Irewole da ke jihar Osun, Dr Esther Okunola, ce ta sanar da rasuwar sarkin a wata sanarwa da aka samu a Osogbo a ranar Litinin.

Source: Facebook
Wani Sarki a jihar Osun ya rasu
Sai dai majiyoyi na kusa da fadar sarkin sun ce Oba Falabi ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya a karshen mako, kamar yadda jaridar Punch ta kawo.
A sakon ta’aziyyarta da ta aika, Okunola ta bayyana rasuwar a matsayin “faduwar giwa babba,” tana mai cewa Ikire da daukacin karamar hukumar Irewole sun yi babban rashi
Shugabar karamar hukumar ta ce al'ummar yankin masarautar sun yi rashin uba, wanda hikimarsa, jarumtarsa da shawarwarinsa suka kasance ginshikin hadin kai da cigaba.
An yabi marigayi Oba Olatunde Falabi
Ta ce mulkinsa ya kasance mai cike da zaman lafiya, kare al’adu da kuma jajircewa wajen bunkasa yankin masarautar Ikire
“Jagorancin da marigayin ya yi, ya kara karfafa harkokin gargajiya da al'adu tare da samar da zaman lafiya a tsakanin al’ummarsa.
“Lallai idan giwa babba ta fadi, daji kan girgiza. Mai martaba ya rayu rayuwa ta kima da hidima. Gadon da ya bari na aiki da hidima za su ci gaba da zama abin koyi ga muate a nan gaba," in ji ta.
Hon. Okunola ta kuma mika ta’aziyya ga iyalan gidan sarauta, Majalisar Gargajiya ta Akire da al’ummar Ikire, tana mai hadawa da addu’ar Allah Ya jikansa da rahama.

Source: Facebook
Takaitaccen bayani kan marigayi Sarki
Punch ta ce Oba Falabi, wanda kwararren masanin harkokin magunguna ne, an nada shi a matsayin Akire na Ikire a watan Mayu 1993, inda ya yi sarauta sama da shekaru 30.
A lokacin mulkinsa, garin ya samu ci gaban tattalin arziki da siyasa, ciki har da kafa Kwalejin Harsuna da Ilimin Dan Adam ta Jami’ar Jihar Osun a Ikire, da kuma fitowar Benedict Alabi, dan asalin garin, a matsayin mataimakin gwamnan jihar Osun.
Tsohon mataimakin gwamnan Delta ya rasu
A wani rahoton, kun ji cewa gwamnan Delta, Sheriff Oborevwori, ya bayyana alhininsa kan rasuwar tsohon mataimakin gwamna da aka taba yi a jihar.
Gwamnan ya ce ya samu labarin rasuwar cikin kaduwa da radadi, amma tare da godiya ga Allah kan rayuwa mai cike da hidima da marigayin ya yi wa Osun da Najeriya baki daya.
Oborevwori ya bayyana marigayin a matsayin dan kishin kasa, gogaggen mai ma'aikaci, kuma jajirtaccen dan jam’iyya wanda za a ci gaba da tunawa da ayyukan alherinsa.
Asali: Legit.ng

