Kurunkus: Shugaba Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Rundunar 'Yan Sandan Najeriya
- Shugaba Bola Tinubu ya amince da murabus din Kayode Egbetokun daga matsayin Sufeto Janar na rundunar yan sandan Najeriya
- Shugaban kasa ya mika godiya gare shi bisa jajircewa da hidimar da ya yi wa rundunar yan sanda da Najeriya baki daya
- Bola Tinubu ya kuma sanar da nadin AIG Tunji Disu a matsayin mukaddashin Sufetan Yan Sanda, inda ya ce matakin zai fara aiki nan take
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Mataimakin Sufeto Janar na Yan Sanda (AIG), Tunji Disu, a matsayin Mukaddashin Sufeto Janar na Rundunar Yan Sandan Najeriya (IGP).
Wannan mataki na zuwa ne sa'o'i kadan bayan Kayode Egbetokun ya yi murabus daga kujerar shugaban rundunar yan sanda ta kasa a jiya Litinin.

Source: Twitter
Tinubu ya amince da murabus din Egbetokun
A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya wallafa a shafinsa na X, ya ce Tinubu ya amince da murabus din Egbetokun.
Onanuga ya kuma sanar da cewa shugaban kasa ya nada AIG Disu a matsayin mukaddashin Sufeto Janar, yana mai cewa nadin zai fara aiki ne nan take.
Sanarwar ta ce:
“Shugaba Tinubu ya karbi takardar murabus din Egbetokun a safiyar yau, inda ya yi godiya gare shi bisa shekarun da ya kwashe yana hidima ga Rundunar Yan Sandan Najeriya da ma kasa baki daya.”
“Shugaban kasa ya jinjina wa jajircewarsa, kwarewarsa, da kuma tsayin dakan da ya nuna wajen karfafa tsarin tsaron cikin gida a lokacin mulkinsa.”
An nada Egbetokun ne a watan Yunin 2023, inda yake kan wa’adin shekaru hudu wanda aka tsara zai kare a watan Yunin 2027, daidai da gyararren tanadi na Dokar Yan Sanda.
Dalilin Tinubu na nada AIG Tunji Disu
Onanuga ya kara da cewa Shugaba Tinubu yana da kwarin gwiwar cewa AIG Disu na da gogewar da zai maye gurbin Egbetokun a rundunar yan sanda.

Kara karanta wannan
Babbar magana: Shugaban rundunar 'yan sandan Najeriya ya yi murabus, an ji dalili
"Shugaban kasa na da yakinin cewa gogewar AIG Disu, sanin makamar aiki da kuma bajintarsa wajen jagoranci za su samar da alkibla mai karko ga Rundunar Yan Sandan Najeriya a wannan lokaci mai muhimmanci.”
“Dangane da bin tanadin Dokar Yan Sanda ta 2020, Shugaba Tinubu zai kira taron Majalisar Yan Sanda ta Najeriya nan ba da dadewa ba domin duba batun nada AIG Disu a matsayin cikakken Sufeto Janar na Yan Sanda.
"Bayan nan kuma za a tura sunansa zuwa Majalisar Dattawa domin tantancewa.”
- Bayo Onanuga.

Source: Twitter
Shugaba Tinubu ya sake nanata kudirin gwamnatinsa na bunkasa tsaron kasa, karfafa hukumomi, da kuma tabbatar da cewa Rundunar Yan Sandan Najeriya ta ci gaba da sauye nauyin da kundin tsarin mulki ya dora mata.
Dalilin murabus din Egbetokun
A wani rahoton, kun ji cewa Fadar Shugaban Ƙasa ta tabbatar da cewa Kayode Egbetokun ya ajiye mukaminsa na Sufeto Janar na ‘Yan Sanda (IGP).
Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya bayyana wa Punch cewa Egbetokun ya miƙa takardar murabus dinsa ne a ranar Talata 24 ga watan Fabrairun 2026.
Ya ce Egbetokun ya bayyana cewa ya yanke shawarar ajiye aiki ne domin bai wa iyalansa kulawa, domin suna bukatar hakan a halin yanzu.
Asali: Legit.ng
