NOA Ta Gargadi 'Yan Kasuwa, Ta Gano Abubuwa 2 da Za Su Kawo Wahala a Watan Ramadan

NOA Ta Gargadi 'Yan Kasuwa, Ta Gano Abubuwa 2 da Za Su Kawo Wahala a Watan Ramadan

  • Hukumar NOA ta bayyana cewa boye kayan abinci da kara farashi ba bisa ka'ida ba na iya jefa mutane a wata sabuwar tsadar rayuwa a watan azumi
  • Sakamakon haka, NOA ta gargadi yan kasuwa da su gujewa wadannan abubuwa biyu domin kaucewa tashin farashin kayan abinci
  • Shugaban NOA na kasa, Lanre Issa-Onilu ya ce ɓoye kaya da gangan na rushe ƙoƙarin da ake yi na daidaita tattalin arziki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA), ta gargaɗi ’yan kasuwa da su guji ɓoye kayan abinci da kuma ƙara farashi ba bisa ƙa’ida ba a lokacin watan Ramadan da kuma azumin Kiristoci na Lent.

Wannan gargadi na kunshe ne a wata sanarwa da Shugaban ahukumar NOA na kasa, Lanre Issa-Onilu, ya fitar a ranar Alhamis, 19 ga watan Fabrairu, 2026.

Kara karanta wannan

Katuwar bishiya ta kifo kan fasinjoji a mota, ta danne su sun mutu

Kayan abinci.
Kayan abinci irinsu Wake, Gyada da makamantansu a kasuwa Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

NOA ta gano makircin yan kasuwa

A rahoton da The Cable ta dauko, ya ce hukumar ta samu rahotanni cewa wasu ’yan kasuwa na ɓoye muhimman kayayyakin abinci da ake yawan amfani da su a lokacin azumi.

Issa-Onilu ya ce a bayanan da suka samu, 'yan kasuwa na boye kayan abincin ne domin su haifar da ƙarancin kaya a kasuwa tare da ƙara farashi.

Ya bayyana wannan dabi’a a matsayin abin da ke kawo tangarda ga tattalin arziki kuma hakan rashin ɗa’a ne musamman a lokacin da ake bukatar tausayi, sadaukarwa da kula da juna.

“Wannan lokaci ne da ake bukatar tausayi, sadaka da jin ƙai ga marasa galihu. Abin takaici ne yadda wasu ke anfani da wannan lokaci na ibada domin neman riba mai yawa a kan talakawa,” in ji shi.

Illar boye kaya ga tattalin arzikin kasa

Shugaban NOA ya ce ɓoye kaya da gangan na rushe ƙoƙarin da ake yi na daidaita tattalin arziki, yana ƙara hauhawar farashi tare da tsananta wahalar da mutane ke fuskanta, cewar Daily Post.

Kara karanta wannan

'Yan daba sun yi wa 'yan APC jina jina a wajen taro, wasu sun rasu

Ya ƙara da cewa gudanar da kasuwanci cikin adalci wajibi ne na ƙasa da kuma na ɗabi’a, yana mai jaddada cewa gaskiya, daidaito da arahar farashi sun dace da ƙimar ƙasa da koyarwar addini.

Issa-Onilu ya buƙaci ƙungiyoyin ’yan kasuwa da na kasuwanni su tabbatar da bin doka da oda a tsakanin mambobinsu, tare da haɗin gwiwa da hukumomin da abin ya shafa domin tabbatar da bin doka.

Shugaban hukumar NOA.
Shugaban hukumar NOA ta kasa, Lanre Issa-Onilu Hoto: NOA
Source: Twitter

Hukumar NOA ta tashi tsaye

Ya kuma sake jaddada aniyar NOA na ci gaba da shirye-shiryen wayar da kai a jihohi da ƙananan hukumomi domin ƙarfafa ɗabi’a mai kyau, tattalin arziki da haɗin kan ƙasa.

Hukumar ta ce za ta ci gaba da sa ido kan al’amura tare da tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin kare jin daɗin al’umma da kuma tabbatar da martabar ƙasa.

Hauhawar farashi ya ragu a Najeriya

A wani rahoton, kun ji cewa hukumar NBS ta tabbatar da raguwar hauhawar farashin kayan abinci da sauran kayayyakin amfani a watan Janairu, 2026.

Hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ta bayyana cewa alkaluman hauhawar farashi ya yi ka zuwa kashi 15.10 cikin 100 a watan Janairu da ya gabata.

Manyan sassan da suka fi bada gudummawa ga raguwar hauhawar farashin sun haɗa da abinci da abin sha marasa giya (6.04%), gidajen cin abinci da masauki (1.95%), da sufuri (1.61%).

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262