Gwamna Ya Tausayawa Ma'aikata, Ya Masu Wata Garaɓasa a Wurin Aiki saboda Ramadan
- Gwamna Bala Mohammed ya rage awannin aikin ma'aikatan Bauchi inda za su rika tashi da karfe 3:00 na yamma a watan Ramadan
- A cewar gwamnan, wannan matakin zai ba ma'aikata Musulmi damar yin ibada a cikin nutsuwa da kuma halartar tafsiran Al-Kur'ani
- A gefe guda, Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq ya taya Musulmi da Kirista murnar fara azumin Ramadan da na Lent a rana daya
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Bauchi - Gwamnan Bauchi, Bala Mohammed, ya tausaya wa ma'aikatan jiharsa yayin da aka fara azumin watan Ramadan na shekarar 2026.
Mai girma Bala Mohamed ya amince da rage lokutan tashi daga aiki ga ma'aikatan gwamnatin jihar a duk tsawon lokacin azumin Ramadan na bana.

Source: Twitter
Gwamna ya ji tausayin ma'aikata a Bauchi
Wannan umarni na kunshe a cikin sanarwar da daraktan harkokin ma'aikata a ofishin shugaban ma'aikata, Ismail Ibn L Garam, ya fitar a ranar Talata, in ji rahoton Daily Trust.
Sanarwar, mai kwanan wata 17 ga Fabrairu, 2026, ta bayyana cewa wannan mataki ne na ba wa ma'aikata Musulmi damar gudanar da ibadu cikin natsuwa.
Hakazalika, gwamnan jihar ya ce ma'aikata Musulmi za su samu isasshen lokacin halartar tafsiran Al-Kur'ani a watan Ramadan.
Sabacbin lokutan tashi daga aiki a Bauchi
Sanarwar ta bayyana cewa, Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed, ya amince ma'aikata su riƙa tashi daga aiki a lokacin azumin Ramadan na 1447AH/2026 kamar haka:
- Litinin zuwa Alhamis: Za a riƙa tashi da ƙarfe 3:00 na yamma.
- Ranar Juma'a: Lokacin tashi yana nan a ƙarfe 1:00 na rana kamar yadda aka saba.
An kuma buƙaci ma'aikata da su yi amfani da wannan lokaci mai tsarki wajen gudanar da addu'o'in neman ci gaba, zaman lafiya, da haɗin kai a jihar Bauchi da kuma Najeriya baki ɗaya.
Sakon Gwamna ga Musulmi da Kirista
A ɓangare guda, Gwamnan Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya taya al'ummar Musulmi da Kirista murnar fara azumin Ramadan da kuma na Lent a yau Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026.

Kara karanta wannan
Kurunkus: Gwamna Abba ya bayyana ainihin dalilinsa na komawa APC a gaban Shettima

Source: Twitter
Gwamnan ya lura cewa fara azumin addinan biyu a rana ɗaya ya ƙara jaddada buƙatar kowa ya yi aiki tare don samar da zaman lafiya da kuma yaƙi da duk wani mugun nufi da zai dakile ci gaban ƙasa.
Jaridar Tribune ta rahoto Abdulrahman Abdulrazaq ya ce:
"Azumi yana buɗe wa ɗan adam wata kofa ta musamman ta kusanci ga Mahalicci ta hanyar nisantar zunubai, bayar da sadaka, da ayyukan alheri."
Ya kuma buƙaci mabiya addinan biyu da su yi aiki tare da gwamnati wajen inganta jin daɗin rayuwar jama'a tare da addu'ar samun sauƙi a cikin yanayin da ƙasar take ciki.
Ramadan: Gwamna zai kashe N1bn a ciyarwa
A wani labari, mun ruwaito cewa, gwamnatin Sokoto ta ware Naira biliyan daya domin ciyar da masu azumi a Ramadan na shekarar 2026 da muke ciki.
Gwamna Ahmed Aliyu ya kaddamar da shirin a Hukumar Tarihi ta jihar, yana cewa an kara cibiyoyin ciyarwa daga 155 zuwa 170.
Shirin, wanda aka fara tun zamanin tsohon gwamna Aliyu Wamakko, na ci gaba da tallafa wa dubban mabukata domin rage radadin talauci.
Asali: Legit.ng
