Babbar Magana: Ganduje Ya Yi Magana kan Batan Dadiyata, Ya Maida Martani ga El Rufai
- Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya tanka wa tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai kan batun bacewar Abubakar Idris, watau Dadiyata a 2019
- Tsohon shugaban jam'iyyar APC na kasa ya bayyana zargin da Malam El-Rufai ya jingina masa a matsayin mara tushe ballantana makama
- Ganduje ya nuna tausayawa ga iyalan Abubakar Idris 'Dadiyata', yana mai cewa abin da ya kamata a mayar da hankali a kai shi ne gano gaskiya
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Tsohon shugaban APC na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya yi kira da a binciki tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, bayan da ya danganta shi da ɓacewar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.
Ganduje, tsohon gwamna a jihar Kano, ya bayyana zargin da Malam El-Rufai ya jingina masa a matsayin “marar tushe, rashin hankali, da kuma yunƙurin kauce wa alhakin abin da ya faru a Kaduna.”

Source: Twitter
Premium Times ta tattaro cewa hakan na kunshe ne a wata sanarwa da tsohon Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Kano, Muhammad Garba, ya sanya wa hannu.
Zargin da El-Rufai ya jingina wa Ganduje
Tun da farko, El-Rufai ya yi iƙirarin cewa an sace Dadiyata ne daga gidansa da ke Kaduna ta hannun ‘yan sanda da aka turo daga Jihar Kano, a lokacin da Ganduje ke gwamna.
A wata hira da ya yi da Arise TV ranar Juma’a, El-Rufai ya ce Dadiyata ba mai sukar gwamnatinsa ba ne kamar yadda ake zato, sai dai mai caccar gwamnatin Ganduje ne.
Ganduje ya maida martani ga El-Rufai
A nasa ɓangaren, Ganduje ya musanta zargin gaba ɗaya, yana mai cewa Dadiyata yana zaune kuma yana aiki ne a Kaduna, inda aka fi saninsa da sukar gwamnatin jihar a lokacin.
Muhammad Garba ya ce:
“Kowa a Kaduna ya san irin sukar da yake yi da kuma wanda yake nufi da ita.”
Ya ƙara da cewa alhakin tsaron Dadiyata a lokacin yana hannun gwamnatin Kaduna da hukumomin tsaro na tarayya da ke aiki a jihar.

Source: Twitter
Ganduje ya tausaya wa iyalan Dadiyata
Sanarwar ta buƙaci a yi taka-tsantsan da kalaman El-Rufai, tana mai cewa irin waɗannan manyan zarge-zarge dole ne su kasance tare da hujjoji masu ƙarfi, ba kalaman siyasa ba.
Ganduje ya nuna tausayawa ga iyalan Dadiyata, yana mai cewa abin da ya kamata a mayar da hankali a kai shi ne gano gaskiya ta hanyar bin doka da tsari.
“Iyalansa suna buƙatar sanin gaskiya. Ba su cancanci a mayar da wannan lamari mai raɗaɗi ya zama abin jayayyar siyasa ba,” in ji Garba.
A ƙarshe, ya buƙaci duk wanda ke da sahihin bayani kan lamarin ya miƙa shi ga hukumomin da suka dace, yana jaddada cewa dole ne a gina irin wannan zargi bisa hujjoji da bin doka, ba zato ba.
El-Rufai ya gano wanda ya sa a kama shi
A wani labarin, kun ji cewa tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi ikirarin cewa sun saurari wayar mai ba shugaban kasa shawara kan taaro, Nuhu Ribadu.
Malam El-Rufai ya kuma zargi Nuhu Ribadu da hannu a yunƙurin kama shi a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a ranar Alhamis.
Sai dai bai gabatar da wata hujja da ke tabbatar da zargin ba, kuma har zuwa yanzu, babu wata sanarwa a hukumance daga Nuhu Ribadu kan zargin.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


