Bayan EFCC, Wata Hukumar Binciken Rashawa Ta Gayyaci El Rufai, Zai Sha Tambayoyi
- Malam Nasir El-Rufai ya tabbatar da cewa zai kai kansa ofishin hukumar ICPC domin amsa gayyatar da ta yi masa
- Lauyan El-Rufai ya bayyana cewa tsohon gwamnan zai fara kai kansa ofishin EFCC ranar Litinin kafin ya je ofishin ICPC
- Wannan na zuwa ne 'yan awanni bayan jami'an tsaro sun yi yunkurin kama tsohon gwamnan a filin jirgin Abuja
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja - Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya tabbatar da cewa zai amsa gayyatar da hukumar ICPC ta yi masa a ranar Laraba, 18 ga Fabrairu.
Wannan na zuwa ne 'yan awanni bayan wasu jami'an tsaro sun yi yunkurin kama El-Rufai a filin jirgin sama na Abuja.

Source: Twitter
El-Rufai zai mika kansa ga ICPC
El-Rufai ya bayyana cewa ya karbi takardar gayyata da ICPC ta aika masa a wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X a ranar Juma'a.
Tsohon Ministan Abuja ya bayyana cewa zai gabatar da kansa a ofishin hukumar kamar yadda aka tsara domin amsa dukkan tambayoyin da ake masa.
Nasir El-Rufai ya ce:
"Jiya, bayan yunƙurin da aka yi na sace ni wanda ba ayi nasara ba, hukumar ICPC ta kawo mini takardar gayyatar su."
Ya ƙara da cewa:
"Lauyana ya riga ya rubuta takarda domin tabbatar da cewa zan bayyana a ofishin ICPC ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026."
El-Rufai ya ce jami'an tsaro sun matsa masa
Mai magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye, ya yi zargin cewa jami'an sun yi ƙoƙarin kama El-Rufai ba tare da nuna takardar gayyata ta hukuma ba.
Tsohon gwamnan na Kaduna ya ce:
"Sun kwace fasfo ɗina na fita ƙasashen waje a lokacin dambarwar, wanda hakan ya sa magoya baya suka nuna fushinsu."
Haka zalika, lauyansa Ubong Akpan ya yi Allah-wadai da yunƙurin kama shi, inda ya bayyana lamarin a matsayin wani mataki da ya saɓa wa doka.

Source: Twitter
Matsayar lauyoyi kan bin dokar kasa
Lauyan ya bayyana cewa wanda yake karewa a shirye yake ya ba da haɗin kai, amma dole ne a bi dukkan ƙa'idojin shari'a yadda ya kamata, in ji rahoton Punch.
Akpan ya bayyana abin da ya faru a filin jirgin a matsayin keta haƙƙin ɗan adam da kuma saba wa tsarin aikin hukumomin tsaro a Najeriya.
Ya kuma bayyana cewa hukumar EFCC ta riga ta aika wa El-Rufai gayyata tun yana ƙasar waje, kuma ya amince zai kai kansa.
A halin yanzu, wasu na kusa da El-Rufai, Amadu Sule da Jimi Lawal, suna fuskantar tuhume-tuhume na zamba da halatta kuɗaɗen haram daga ICPC.
El-Rufai zai kai kansa ofishin EFCC
Tun da fari, mun rahoto cewa, Nasir El-Rufai ya ce zai kai kansa ofishin hukumar EFCC a ranar Litinin, domin amsa gayyatar da ta yi masa
Yayin da yake a ƙasar, EFCC ta aika da takardar gayyata zuwa gidansa a watan Disambar shekarar 2025, wanda hakan ya jawo raɗe-raɗin cewa za a iya kama shi.
Jama'a na dakon ganin yadda wannan ziyara ta El-Rufai zuwa ofishin EFCC za ta kasance a ranar Litinin mai zuwa, 16 ga Fabrairu, 2026.
Asali: Legit.ng

