Bayan EFCC, Wata Hukumar Binciken Rashawa Ta Gayyaci El Rufai, Zai Sha Tambayoyi

Bayan EFCC, Wata Hukumar Binciken Rashawa Ta Gayyaci El Rufai, Zai Sha Tambayoyi

  • Malam Nasir El-Rufai ya tabbatar da cewa zai kai kansa ofishin hukumar ICPC domin amsa gayyatar da ta yi masa
  • Lauyan El-Rufai ya bayyana cewa tsohon gwamnan zai fara kai kansa ofishin EFCC ranar Litinin kafin ya je ofishin ICPC
  • Wannan na zuwa ne 'yan awanni bayan jami'an tsaro sun yi yunkurin kama tsohon gwamnan a filin jirgin Abuja

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya tabbatar da cewa zai amsa gayyatar da hukumar ICPC ta yi masa a ranar Laraba, 18 ga Fabrairu.

Wannan na zuwa ne 'yan awanni bayan wasu jami'an tsaro sun yi yunkurin kama El-Rufai a filin jirgin sama na Abuja.

El-Rufai ya karbi takardar gayyata daga hukumar ICPC
Malam Nasir El-Rufai, da ginin ofishin hukumar ICPC da ke Abuja. Hoto: @elrufai, @icpcnigeria
Source: Twitter

El-Rufai zai mika kansa ga ICPC

El-Rufai ya bayyana cewa ya karbi takardar gayyata da ICPC ta aika masa a wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X a ranar Juma'a.

Kara karanta wannan

Shekaru 7 da ɗauke Dadiyata, El Rufai ya faɗi gaskiyar abin da ya sani

Tsohon Ministan Abuja ya bayyana cewa zai gabatar da kansa a ofishin hukumar kamar yadda aka tsara domin amsa dukkan tambayoyin da ake masa.

Nasir El-Rufai ya ce:

"Jiya, bayan yunƙurin da aka yi na sace ni wanda ba ayi nasara ba, hukumar ICPC ta kawo mini takardar gayyatar su."

Ya ƙara da cewa:

"Lauyana ya riga ya rubuta takarda domin tabbatar da cewa zan bayyana a ofishin ICPC ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026."

El-Rufai ya ce jami'an tsaro sun matsa masa

Mai magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye, ya yi zargin cewa jami'an sun yi ƙoƙarin kama El-Rufai ba tare da nuna takardar gayyata ta hukuma ba.

Tsohon gwamnan na Kaduna ya ce:

"Sun kwace fasfo ɗina na fita ƙasashen waje a lokacin dambarwar, wanda hakan ya sa magoya baya suka nuna fushinsu."

Haka zalika, lauyansa Ubong Akpan ya yi Allah-wadai da yunƙurin kama shi, inda ya bayyana lamarin a matsayin wani mataki da ya saɓa wa doka.

El-Rufai ya ce zai mika kansa ga ICPC awanni 48 bayan ya gana da EFCC.
Mallam Nasir El-Rufai, zaune a kan kujerar Gwamnan Kaduna a ranar 15 ga Yuni, 2019. Hoto: @elrufai
Source: Twitter

Matsayar lauyoyi kan bin dokar kasa

Lauyan ya bayyana cewa wanda yake karewa a shirye yake ya ba da haɗin kai, amma dole ne a bi dukkan ƙa'idojin shari'a yadda ya kamata, in ji rahoton Punch.

Kara karanta wannan

El Rufai zai tsaya takarar shugaban Najeriya a 2027? Tsohon gwamna ya bada amsa

Akpan ya bayyana abin da ya faru a filin jirgin a matsayin keta haƙƙin ɗan adam da kuma saba wa tsarin aikin hukumomin tsaro a Najeriya.

Ya kuma bayyana cewa hukumar EFCC ta riga ta aika wa El-Rufai gayyata tun yana ƙasar waje, kuma ya amince zai kai kansa.

A halin yanzu, wasu na kusa da El-Rufai, Amadu Sule da Jimi Lawal, suna fuskantar tuhume-tuhume na zamba da halatta kuɗaɗen haram daga ICPC.

El-Rufai zai kai kansa ofishin EFCC

Tun da fari, mun rahoto cewa, Nasir El-Rufai ya ce zai kai kansa ofishin hukumar EFCC a ranar Litinin, domin amsa gayyatar da ta yi masa

Yayin da yake a ƙasar, EFCC ta aika da takardar gayyata zuwa gidansa a watan Disambar shekarar 2025, wanda hakan ya jawo raɗe-raɗin cewa za a iya kama shi.

Jama'a na dakon ganin yadda wannan ziyara ta El-Rufai zuwa ofishin EFCC za ta kasance a ranar Litinin mai zuwa, 16 ga Fabrairu, 2026.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com