‘Ba Shi Kadai Ya Kafa Shari’a ba’: An ‘Gano’ Shirin Amurka kan Siyasar Kwankwaso
- Mai fashin baki a siyasa, Mahdi Shehu ya yi magana kan ayyana Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin mai tsattsauran ra’ayi
- Ya danganta ayyana Kwankwaso da wasu sauye-sauyen siyasa da suka faru, ciki har da sauya sheƙar gwamnan Kano da tattaunawar takarar mataimaki
- Mahdi Shehu ya yi zargin cewa ana iya yin irin wannan sharri ga Atiku Abubakar, Nasir El-Rufai da sauran jagororin adawa
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Wani mai fashin baki kan harkokin siyasa, Mahdi Shehu, ya yi magana game da korafin da Amurka ta yi kan Rabiu Kwankwaso.
Mahdi ya bayyana cewa ayyana Rabiu Musa Kwankwaso, a matsayin mai tsattsauran ra’ayin addini wani shiri ne da aka tsara domin rage masa karfi a siyasa da kuma raunana adawa.

Source: Facebook
'Shirin da Amurka ta yi kan Kwankwaso'
Mahdi Shehu ya bayyana haka ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce ana yi wa jagororin adawa lakabi da nufin bata musu suna a idon duniya.
Mahdi ya bayyana cewa ba kuskure ba ne ayyana Kwankwaso a matsayin mai tsauttsauran ra'ayin addini inda ya ce bai da tarihin haka.
Ya ce:
“Gaskiyar magana, ana ayyana Kwankwaso a matsayin mai tsattsauran ra’ayi alhali an san ba shi da wannan tarihin, ba kuskure ba ne, wani tsari ne na rage masa tasiri a siyasa.”
Sannan ya ce akwai wata alaka ta tsakanin wasu muhimman abubuwan siyasa da kuma ayyana Kwankwaso da aka yi.

Source: Twitter
Zargin dalilin kakaba wa Kwankwaso 'sharri'
Ya misalta cewa makonni biyu bayan wasu tattaunawa na kasa da kasa da sauyin sheƙar gwamnan Kano, an bayyana Rabiu Kwankwaso a matsayin mai tsattsauran ra’ayi.
Ya kara da cewa idan sanya hannu kan dokar Shari’ar laifuffuka a Kano ne dalili, to ya kamata a kira duk gwamnonin Arewa da suka rattaba hannu kan dokokin Shari’a a lokacin Olusegun Obasanjo da sunan masu tsattsauran ra’ayi.
“Idan ayyana Kwankwaso a matsayin ‘mai tsattsauran ra’ayin Musulunci’ ya samo asali ne daga rattaba hannunsa kan Dokar Hukunta Laifuka ta Shari’a a Kano lokacin yana gwamna, to hakan na nufin dukkan gwamnonin jihohin Arewa da suka sanya hannu kan dokokin Shari’a a lokacin da kuma bayan mulkin Obasanjo su ma za a kira su masu tsattsauran ra’ayi. Wannan ya hada da gwamnonin Zamfara, Katsina, Sokoto, Kebbi, Kaduna, Bauchi, Jigawa, Gombe, Borno da Yobe."
- Cewar Mahdi
Mahdi Shehu ya kuma ambaci cewa makonni biyu bayan wasu manyan ‘yan siyasa sun gana da Kwankwaso, sai aka sake jaddada wannan sharri a kansa, abin da ya ce ba daidaito ba ne illa wata dabara ta siyasa kafin zaben 2027.
Ya yi gargadin cewa ana iya yin irin wannan sharri kan wasu jagororin adawa kamar Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai, ta hanyar jingina musu daukar nauyin ta’addanci.
A cewarsa, duk wadannan zarge-zarge da ake jingina wa jagororin adawa, na cikin abin da ya kira yaki da adawa wanda daga karshe gaskiya za ta bayyana.
Kwankwaso: Kwankwasiyya ta tura sako ga Amurka
Mun ba ku labarin cewa Kwankwasiyya ta aika sako Amurka bayan sanya sunan Kwankwaso a jerin wadanda kasar ke zargi da hannu a tauye hakkin addini a Najeriya.
Tafiyar Kwankwasiyya ta bayyana cewa ba a jihar Kano kadai aka kaddamar da shari'a ba, don haka ware mutum daya ba adalci ba ne.
Ta bukaci majalisar dokokin Amurka ta gaggauta cire sunan Kwankwaso daga cikin kudirinta domin hakan na iya yi masa illa a siyasance.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

