Abba Hikima: Jama'a Sun Ƙara Tara wa Haruna Kuɗi bayan Kashe Matarsa da Yara 6
- Bayan tallafin farko na Naira miliyan 25, jama’a sun ci gaba da turawa Mal. Haruna Bashir kudi domin rage masa radadi
- Haruna Bashir na ya shiga tashin hankali bayan wani Umar da matasa biyu sau shiga gidansa, tare da kashe iyalinsa duka
- A tashin farko, jama'a sun bayar da gudunmawar N25m ta hannun fitaccen lauya Abba Hikima, yanzu kuma aka samu kari
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Kano – Bayan tallafin farko da jama’a suka baiwa Malam Haruna Bashir Naira miliyan 25, mutane sun ci gaba da tura masa gudunmawa.
Fitaccen lauya, Barista Abba Hikima ne ya tabbatar da haka, inda ya bayyana cewa tuni aka hada wasu kudin bayan an ba shi taron farko

Kara karanta wannan
Rashin imani: Yadda 'yan ta'adda suka kira Sallah, suka kashe duk wanda ya zo Masallaci

Source: Facebook
A sakon da Abba Hikima ya wallafa a shafinsa na Facebook, jama'a sun kara tura N453,000 domin a mika wa Haruna Bashir.
Jama'a sun kara taimakawa Haruna Bashir
Daga cikin kudin da aka samu, Malam Haruna Bashir ya yi amfani da wani bangare wajen tallafawa dangin matarsa da sauran yan’uwansa.
Barista Abba Hikima ya bayyana cewa Haruna Bashir ya dauki matakin ne kamar yadda jamaa da dama suka bayar da shawara.

Source: Facebook
Magidancin dai ya gamu da iftila'i bayan wasu bata-garin matasa uku, wanda dangin matar ne sun shiga gidansa, tare da kashe Fatima Abubakar da yaransu shida.
Lamarin ya daga hankulan jama'a da shugabannin al'umma, kuma yanzu haka gwamnatin Kano ta fara shari'a da matasan da suka amsa kisa.
Jama'a sun yi wa Haruna Bashir addu'a
Mutanen da ke bin shafin Abba Hikima sun bayyana jin dadi a kan yadda jama'a ke ci gaba da taimakon Haruna Bashir da ya rasa iyalansa baki daya.
Fatima Halilu Rabiu ta ce:
"Masha Allahu Allah ya jikan su da Rahma ya sakawa duk wadanda suka taimaka da alkairi."
Fadima Usman ta bayyana cewa:
"Ni a gani na da an hakura da wallafa maganan kudin nan haka, saboda kar abin yayi karfafa wa masu mugun tunani a maida abin hanyar neman arziki. Allah Ya kyauta, Allah jikan su Ya kara wa makusantan su hakuri."
Musbahu Adamu Aminu ya bayyana cewa:
"Allah ya biya ka da gidan aljanna, hakik da za mu samu irin ku a matsayin shugabanni da wallahi mun dace saboda irin yadda ka ke shiga da jibintar alamuran wanda yake cikin neman agaji. Muna addu'ar Allah ya kara maka sutura da karfin guiwa."
Daurawa ya ziyarci Haruna Bashir
A wani labarin, kun ji cewa
Asali: Legit.ng
