Abin Tausayi: Halin da Mutanen da Aka Sace Suna cikin Ibada Suka Shiga a Hannun Yan Bindiga
- A jiya Alhamis G wamnatin Kaduna ta tabbatar da dawowar ragowar kiristocin da aka sace a coci uku a garin Kurmin Wali
- 'Yan bindiga sun kai farmaki ne a lokacin da mutane ke tsakiyar ibada ranar Lahadi, inda suka tafi da masu ibada fiye da 177 zuwa daji
- Bayan ceto mutanen, sun fara bayyana irin ukuba da azabar da suka sha hannun 'yan bindigar na tsawon makonni biyu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kaduna, Nigeria - Gwamnatin Kaduna ta tabbatar da cewa an ceto duka ragowar kiristocin da 'yan bindiga duka sace a Kurmin Wali da ke karamar hukumar Kajuru.
Wasu daga cikin mutanen da aka sace suna tsakiyar ibada sun yi bayanin mummunan halin da suka shiga da abubuwan da 'yan bindiga suka rika masu a cikin daji.

Kara karanta wannan
Masu ibada da aka sace a Kaduna, sun fadi yadda rayuwa ta kasance a hannun 'yan bindiga

Source: Facebook
Leadership ta tattaro cewa an sace mutanen ne tun ranar 18 ga watan Janairun 2026 yayin da suke tsaka da ibada, inda aka ceto su ranar Alhamis bayan kwashe mako biyu a tsare.
Halin da suka shiga a hannun 'yan bindiga
Daya daga cikin waɗanda suka dawo, Hosea Madami, ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa sun fuskanci cin zarafi da azaba iri daban-dabanl'okacin da suke hannun masu garkuwa.
“Mun sha wahala sosai a daji. Sun doke ni a kaina da hannuwana, suna ciyar da mu kamar karnuka; abincin ma kaɗan suke zuba mana a hannu. Babu gishiri, don haka abincin ba shi da wani ɗanɗano,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa an tilasta musu yin tafiyar ƙasa na kwanaki shida a cikin daji ana dukan su da gora.
Yadda aka azabtar da mutanen da yunwa
Wata mata mai suna Rebecca Josiah, daga cikin wadanda aka ceto, ta bayyana cewa yunwa ita ce babban abin da ya fi addabar su.
“Sau huɗu kawai na ci abinci a cikin mako biyu da muka yi a daji. Suna ba mu kunu ko tuwo a hannunmu. Idan abincin yana da zafi sosai, sai dai ka zuba shi a jikin tufafinka ka ci."
Ta ƙara da cewa sun yi tafiyar kwanaki ba takalmi, wanda hakan ya sa ƙafafunsu suka kumbura sakamakon taka ƙaya, yayin da ƙananan yara suka dinga kuka saboda tsananin yunwa.
Wata mata da ta buƙaci a sakaya sunanta ta ce ba a ba su damar yin wanka ba ko sau ɗaya, duk da cewa sun kwana kusa da kogi kuma idan mutum ya yi tari ko yara suka yi kuka, ‘yan bindigar suna dukan mutum, musamman maza.
Wata mai juna biyu, Theresa Irimiya, ta ce an sauƙaƙa mata saboda yanayinta, inda aka ƙyale ta ba a doke ta ba, sannan aka sallame ta da wuri tare da wasu yara.

Source: Facebook
An sako sauran mutanen Kaduna da aka sace
A wani rahoton, kun ji cewa yan bindiga sun sako ragowar kiristocin da suka yi garkuwa da su suna tsakiyar ibada a coci a garin Kurmin Wali, jihar Kaduna.
Wani jagoran al'umma wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya shaida cewa an sako mutanen ne a daren jiya Laraba, kuma an wuce da su zuwa gudan gwamnatin Kaduna.
Har yanzu ba a tabbatar da ko an biya kuɗin fansa ba, ko kuma an ba wa masu garkuwar babura 17 da suka nema a baya kafin su sako mutanen ba.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

