Babbar Magana: Trump Ya Sake Gargaɗin Khamenei, Ya Faɗi Ɓarnar da Ya Yi wa Iran

Babbar Magana: Trump Ya Sake Gargaɗin Khamenei, Ya Faɗi Ɓarnar da Ya Yi wa Iran

  • Shugaban Amurka Donald Trump ya gargadi jagoran Iran Ayatollah Ali Khamenei yayin da rikicin Amurka da Iran ke kara tsananta
  • Trump ya ce Amurka na kara jibge kayan soji a kusa da Iran, yayin da tattaunawar diflomasiyya ke fuskantar barazana saboda rashin jituwa
  • Shugaban ya yi ikirarin cewa hare-haren Amurka sun lalata cibiyoyin nukiliyar Iran, yana mai cewa hakan ya rage barazanar Iran a duniya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Washington DC, US - Shugaban Amurka Donald Trump ya tura gargadi na musamman ga jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei.

Donald Trump ya gargade shi da ya “ji tsoro” yayin da dangantaka tsakanin kasashen biyu ke kara tabarbarewa a halin yanzu.

Trump ya tura gargadi ga Ayatullah Khamenei
Jagoran addini a Iran, Ayatullah khamenei da Shugaba Donald Trump. Hoto: @RealDonaldTrump, @Khamenei_ir.
Source: Getty Images

Gargadin da Trump ya yi wa Ayatullah Khamenei

Trump ya bayyana hakan ne a wata hira da yan jaridu da CNN ta bibiya a ranar Laraba 4 ga watan Fabrairun 2026 da muke ciki.

Kara karanta wannan

An kashe Musulmai 75 saboda kin karbar bakuwar akida a Kwara

Shugaba Trump ya ce ya kamata Khamenei ya tsorata sosai, saboda abin da zai fuskanta daga Amurka wanda yanzu alakarsu ta kara tsami.

Wannan gargadi ya zo ne yayin da Amurka ke kara tara sojoji da kayan yaki a kusa da Iran, tare da la’akari da daukar matakan soja domin raunata karfin da kasar ke da shi.

Duk da haka, Trump bai rufe kofar sulhu ba, sai dai tattaunawar da aka shirya yi tsakanin kasashen biyu na fuskantar rashin tabbas kan sharuddan zaman.

Shugaban ya ce barazanar da ya rika yi wa Iran ta taimaka wajen karfafa masu zanga-zangar cikin gida, ko da ba tare da shiga kai tsaye ba.

Ya ce:

“Mun tsaya musu. Kasar ta rikice yanzu saboda mu. Mun kai hari, mun lalata cibiyoyin nukiliyarsu gaba daya."
Trump ya fadi illar da ya yi ga Iran
Shugaba Donald Trump na Amurka yayin kamfen siyasa. Hoto: @RealDonaldTrump.
Source: Twitter

Yadda Amurka ta lalata cibiyoyin nukiliyar Iran

Trump ya kara da cewa da ba a lalata shirin nukiliyar Iran ba, da ba za a samu zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya ba, cewar France 24.

Ya bayyana cewa kasashen Larabawa sun daina jin tsoron Iran bayan harin, yana mai cewa an kawo karshen barazanar da Iran ke yi musu.

Kara karanta wannan

Tinubu ya tura bataliyar sojoji Kwara bayan kashe Musulmai sama da 100

Trump ya kuma yi ikirarin cewa Iran na kokarin sake farfado da shirin nukiliyarta a wasu wurare daban-daban a kasar da ta mallaka.

Ya ce Amurka ta gano shirin, inda ya gargadi Iran da cewa duk wani sabon yunƙuri zai jawo musu mummunan martani daga Amurka.

Amurka ta harbo jirgin leken asirin Iran

An ji cewa sojojin Amurka sun ce sun harbo wani jirgin leƙen asirin Iran bayan ya kusanci jirgin ruwan yaki na USS Abraham Lincoln wanda ya sake tarwatsa alakar da ke tsakanin kasashen biyu.

Lamarin ya faru ne a daidai lokacin da ake zargin cewa sojojin kasar Iran sun tsoratar da wani jirgin kasuwanci mai tutar Amurka a mashigar Hormuz.

Hakan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da samun takun saka a dangantaka tsakanin Amurka da Iran kan batun tsaro da shirin mallakar makamin nukiliya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.