Musulunci Ya Yi Rashi: Farfesa kuma Malamin Addini Ya Yi Bankwana da Duniya
- An tabbatar da rasuwar fitaccen malamin Musulunci a Ilorin da ke Jihar Kwara, a ranar Juma’a 30 ga Janairu, 2026
- Gwamnan Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya nuna alhini tare da aikawa da sakon ta’aziyya ga Sarkin Ilorin, shugabannin Musulmi da iyalan marigayin
- Gwamnatin Kwara ta ce marigayin ya bar gagarumar tarihi a ilimi da zaman lafiya, tare da roƙon Allah ya sanya shi a Aljannar Firdaus
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Ilorin, Kwara - Duniyar Musulunci ta yi babban rashi da aka sanar da rasuwar malamin addini kuma Farfesa a jihar Kwara.
An tabbatar da rasuwar Farfesa Yusuf Lanre Badmus a ranar Juma'a 30 ga watan Janairun 2026 da muke ciki.

Source: Facebook
Malamin Musulunci ya rasu a Kwara
Hakan na cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran gwamnan Kwara, Rafiu Ajakaye ya sanyawa hannu wanda gwamnatin jihar ta wallafa a shafin Facebook.
Sanarwar ta ce gwamnatin Kwara ta nuna jimami kan rasuwar malamin wanda ya ba da gudunmawa ga al'umma da kuma addinin Musulunci.
Gwamnan Abdulrahman Abdulrazak ya tura sakon ta'aziyya ga iyalan marigayin, Sarkin Ilorin, shugabannin Musulmi da jihar Kwara baki daya.
Addu'o'i da gwamnan Kwara ya yi
Ya roki Ubangiji ya gafarta masa kuma ya saka masa da gidan aljanna firdausi da kuma kare iyalansa baki daya.
A cikin sanarwar, gwamnatin Kwara ta ce:
"Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana alhininsa kan rasuwar Farfesa Yusuf Lanre Badmus, fitaccen malamin addinin Musulunci kuma jagoran al’umma.
Gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga Mai Martaba Sarkin Ilorin, Dakta Ibrahim Sulu-Gambari, da shugabannin Musulmi a Jihar Kwara, iyalan Markaz, da kuma iyalan marigayin Farfesa Badmus.
Gwamna AbdulRazaq ya ce marigayin ya bar kyakkyawan tarihi a matsayinsa na shahararren malami kuma mai fafutukar zaman lafiya, wanda ya shafe shekaru yana bayar da gagarumar gudunmawa ga Jihar Kwara da Ilorin musamman.
Ya roƙi Allah da ya yi wa Farfesa Yusuf Lanre Badmus rahama, ya sanya shi a Aljannar Firdaus, tare da kiyaye iyalansa a kan alheri."

Source: Twitter
Sarkin Musulmi ya tura sakon jaje
Har ila yau, Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar ya yi jimamin rashin malamin inda ya tura sakon ta'aziyya ga iyalansa da al'ummar Musulmi, cewar NTA News.
Sarkin Musulmi ya bayyana bakin ciki bisa rashin gogaggen malamin inda ya ce tabbas an yi rashin da maye gurbinsa zai yi matukar wahala.
Ya ce babu yadda aka iya da ikon Allah amma mutuwar malamin ta kawo gibi ga Musulunci a Najeriya da duniya baki daya.
An kama malamin Musulunci a Kano
Mun ba ku labarin cewa 'yan sandan Kano sun gurfanar da Sheikh Ibrahim Isa Makwarari a gaban kotu bisa zargin karkatar da filayen gwamnati da na al’umma.
Rahotanni sun nuna cewa an samu ce-ce-ku-ce a zaman kotun bayan lauyansa ya ce akwai wata shari’a makamanciyarta a kasa.
Bayan caccaka tsinke da aka yi a zaman da ya gudana, kotu ta bayar da belin malamin tare da ɗage shari’ar zuwa wani lokaci na daban.
Asali: Legit.ng

