‘Zan ci Gaba da Kaunarsa’: Minista Ta Tuna Kaunar da Ke tsakaninta da Abdulsamad BUA

‘Zan ci Gaba da Kaunarsa’: Minista Ta Tuna Kaunar da Ke tsakaninta da Abdulsamad BUA

  • Ministar harkokin fasaha, al’adu da tattalin arzikin kirkire-kirkire, Hannatu Musawa ta yi magana kan tsohon tsohon mijinta, Abdul Samad Rabiu
  • Hannatu Musawa ta ce Abdulsamad Rabiu zai ci gaba da kasancewa “wani muhimmin bangare na zuciyarta” duk da rabuwar aurensu
  • Ministar ta bayyana cewa ba ta da nadama kan auren da ta yi da shugaban BUA , tana mai cewa dangantakarsu ta koma ta yan uwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja – Hannatu Musawa, ministar harkokin fasaha, al’adu da tattalin arzikin kirkire-kirkire, ta magantu game da tsohon mijinta, Abdul Samad Rabiu.

Hannatu Musawa ta ce shugaban kamfanin BUA, zai ci gaba da kasancewa a zuciyarta har abada saboda alakarsu.

Minista ta tuna soyayyarsu da Abdulsamad BUA
Minista Hannatu Musa Musawa da attajiri Abdulsamad Rabiu. Hoto: @hanneymusawa, @asr_rabiu.
Source: Twitter

Minista ba ta yi nadamar auren BUA ba

Ta bayyana hakan ne yayin wata hira a shirin MIC on Podcast wanda ɗan jarida Seun Okinbaloye ke gabatarwa da Imran Muhammad ya wallafa a X, wanda Legit Hausa ta bibiya.

Kara karanta wannan

Akwai kura: Hannatu Musawa ta yi gargadi kan ajiye Kashim Shettima a 2027

Musawa ta ce ba ta da wata nadama kan auren da ta yi da Rabiu da kuma rabuwar aurensu daga bisani.

Ministar ta jaddada cewa tana alfahari da kanta da kuma zabin rayuwar da ta yi, tana mai cewa dangantakarta da attajirin ɗan asalin Kano ta wuce ta aure zuwa ta yan uwa.

A cewarta:

“Abdul Samad dan uwana ne. Iyalanmu sun hade wuri guda. Mun san juna sama da shekaru 30. Mu yan uwa ne kawai. Muna yawan barkwanci da juna saboda mu yan uwa ne.”

Ta kara da cewa Rabiu ya zama kamar uba, ɗan uwa, aboki kuma mai kareta, tana mai cewa hakan ba ita kaɗai ba ce ke ganin Rabiu haka, mutane da dama na ganin sa a matsayin mai taimako.

Da aka tambayeta game da aurensu na baya, Musawa ta ce har yanzu akwai soyayya da girmamawa a tsakaninsu, duk da cewa ba su ƙara zama miji da mata ba.

“Shi tsohon mijina ne, amma har yanzu dan uwa ne. Mun fito daga al’adar da idan aka hada ku, ko bayan rabuwar aure, kuna cikin rayuwar juna."

Kara karanta wannan

Abubakar Malami ya yi magana game da makamai da DSS ta gano a 'gidansa' na Kebbi

- In ji Hannatu Musawa

Minista ta fadi alakar da ke tsakaninta da Abdulsamad Rabiu
Minista a Najeriya, Hannatu Musa Musawa. Hoto: @hanneymusawa.
Source: Facebook

Minista ta tuna lamarin Allah a rayuwarta

Hannatu Musawa ta kuma bayyana cewa komai yana hannun Allah, inda ta ce wataƙila da ta ci gaba da zama matar Rabiu, da ba za ta kai matsayin da take kai a yau ba.

A ƙarshe, Musawa ta ce har yanzu tana cike da kauna a zuciyarta ga attajirin ɗan kasuwar, tana mai cewa:

“Samad zai ci gaba da kasancewa a zuciyata. Ba shakka yana daga cikin manya a rayuwata. Zan ci gaba da kaunarsa har tsawon rayuwata.”

Minista ta yi gargadi kan sauya Shettima

Mun ba ku labarin cewa ministar harkokin fasaha, al’adu da tattalin arzikin kirkire-kirkire, Hannatu Musawa ta gargadi APC kan sauya tikitin Tinubu–Shettima kafin 2027.

Hannatu Musawa ta ce sauyin zai iya jawo asarar kuri’u a Arewacin Najeriya kuma akwai barazanar cewa ba za a kai labari ba.

Ta bayyana cewa siyasar Arewa tana da tsari da tunani na musamman, kuma dole a nazarce shi da kyau kafin yanke hukunci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.