Kisan Gilla: Lauya Ya ci Gyaran Masu Neman a Yanke wa Su Umar Hukuncin Kisa

Kisan Gilla: Lauya Ya ci Gyaran Masu Neman a Yanke wa Su Umar Hukuncin Kisa

  • Wani lauya a Kano ya ce kiran a gaggauta kashe masu laifin kisan uwa dayayanta shida ya saɓa wa dokokin Najeriya
  • Ya bayyana cewa dole ne kotu ta same wanda ake zargi da laifi, tare da kammala dukkan matakan ɗaukaka ƙara, kafin hukuncin kisa
  • Lauyan ya gargadi jama’a kan ɗaukar doka a hannu, yana mai cewa dole ne a bar shari’a ta bi ƙa’ida duk da tsananin laifi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Wani lauya a jihar Kano, Mubarak Abubakar, ya yi magana game da mutane da ke neman a yanke wa wadanda ake zargi ya kashe iyali guda hukuncin kisa.

Kara karanta wannan

An cafke babban malamin Musulunci, an kai shi kotu kan cinye filaye a Kano

Lauyan ya bayyana cewa kiran da wasu jama’a ke yi na a hanzarta kashe wadanda ake zargi da hallaka Fatima da ’ya’yanta shida a unguwar Dorayi-Chiranci, ya saɓa wa doka.

Lauya ya soki masu neman yanke hukuncin kisa kan Umar
Umar Auwal da iyalin Fatima Abubakar da ya hallaka a Kano. Hoto: Hussaina Abkr.
Source: Facebook

Kisan gilla: Lauya ya gargadi mutane a Kano

Lauyan ya jaddada cewa bisa ƙa’ida, ba za a iya aiwatar da hukuncin kisa ga kowa ba, sai bayan kotu mai ikon shari’a ta same shi da laifi bayan cikakken bincike da sauraron shari’a, cewar Aminiya.

Ya ce doka ta tanadi matakai masu tsauri kafin hukuncin kisa, inda dole ne wanda ake zargi ya samu damar kare kansa a kotu, tare da amfani da dukkan hanyoyin ɗaukaka ƙara da kundin tsarin mulki ya tanada.

A cewarsa, ko bayan kotu ta yanke hukunci, doka ta bai wa wanda aka same shi da laifi damar kai ƙara zuwa Kotun Ɗaukaka Ƙara, sannan daga bisani zuwa Kotun Ƙoli.

Kara karanta wannan

Makwabtan Fatima da aka kashe da yaranta 6 a Kano sun fusata rundunar 'yan sanda

“Har sai an kammala dukkan waɗannan matakai na shari’a, ba bisa doka ba ne a aiwatar da hukuncin kisa."
Ana ci gaba da neman hukunta wadanda suka hallaka Fatima da 'ya'yanta
Haruna Bashir da iyalinsa kafin faruwar iftala'i kansu. Hoto: Hussaina Abkr.
Source: Facebook

'Sharadin yanke hukunci kan laifuffuka' - Lauya

Lauyan ya ƙara da cewa, sai bayan Kotun Ƙoli ta yanke hukunci na ƙarshe, kuma babu sauran damar ƙara ne kawai doka ke ba da izinin aiwatar da hukuncin kisa.

Ya yi nuni da cewa duk da tsananin zafin laifin kisan gilla, dole ne a bar doka ta yi aikinta, domin kauce wa ɗaukar doka a hannu duba da yadda al'umma suka fusata.

Ya kuma yi gargaɗi cewa irin kiran da ake yi na iya haddasa tashin hankali a cikin al’umma, yana mai jaddada cewa adalci na gaskiya ba ya samuwa sai an bi hanyar doka.

Kara karanta wannan

Trump ya tsorata da barazanar kashe shi, ya yi alwashin shafe Iran a duniya

Masanin shari'ar ya yi kokarin nuna yadda doka ta ke aiki ne ba bada kariya ga wadanda ake zargi ba.

Alkawuran da Abba ya yi wa Haruna Bashir

Mun ba ku labarin cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya yi alkawarin biya wa Haruna Bashir, mutumin da aka kashe matarsa da yaransa kudin aikin Hajji da Umrah.

Abba Kabir ya bayyana haka ne a lokacin da ya je ta'aziyya ga mutumin bisa wannan jarabawa da ya tsinci kansa a ciki a unguwar Dorayi da kuma dauka masa alkawura.

Gwamnan ya kuma dauki nauyin auren da Haruna zai yi, tare da ba shi kyautar sabon gida a wata unguwa ta daban a jihar Kano domin samun kwanciyar hankali.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.